Gwamnatin Abba Gida-Gida Ta Soke Lasisin Makarantu Masu Zaman Kansu Gaba Daya a Kano

Gwamnatin Abba Gida-Gida Ta Soke Lasisin Makarantu Masu Zaman Kansu Gaba Daya a Kano

  • Gwamna Abba gida-gida ta jihar Kano ta soke lasisin makarantu masu zaman kansu gaba daya a jihar
  • Wannan na daga cikin matakin da gwamnati ke yi na tabbatar da makarantun sun cike tsari da ka'idoji domin samun ilimi mai inganci
  • An umurci masu makarantun da su sake yin rijista da gwamnatin jihar domin sabonta lasisin su

DUBA NAN: Bibiyi shafin Legit.ng Hausa a kafar TikTok. Kada ka bari bidiyo mai daukar hankali ya wuce ka!

Jihar Kano - Rahotanni sun kawo cewa gwamnatin jihar Kano karkashin jagorancin, Abba Kabir Yusuf, ta soke lasisin makarantu masu zaman kansu a fadin jihar.

Kamar yadda jaridar Kano Focus ta rahoto, mai ba gwamna shawara na musamman kan makarantu masu zaman kansu, Alhaji Baba Abubakar Umar ne ya sanar da hakan a wani taro da ya yi da mamallakan makarantun a ranar Asabar, 12 ga watan Agusta.

Kara karanta wannan

Gwamnonin Arewa Sun Mika Ta’aziyyarsu Ga Masarautar Zazzau Kan Rushewar Masallaci Da Ya Yi Sanadiyar Rasa Rayuka

Gwamnatin Kano ta soke lasisin makarantu masu zaman kansu
Gwamnatin Abba Gida-Gida Ta Soke Lasisin Makarantu Masu Zaman Kansu Gaba Daya a Kano Hoto: Abba Kabir Yusuf
Asali: Facebook

Alhaji Umar ya kuma bayyana cewa ana sa ran gaba daya makarantun za su koma su sake yin rijista domin sabunta lasisinsu, rahoton Aminiya.

Har ila yau, hadimin gwamnan ya jaddada aniyar gwamnatin Abba gida-gida na tsaftace ayyukan makarantu masu zaman kansu tare da tabbatar da sun bi tsari da ka’idoji.

DUBA: Bibiyemu a Instagram don samun labarai masu muhimmanci kai tsaye cikin manhajar

Gwamnatin ta kuma bukaci masu makarantun da su biya kaso 10 na harajin da ke wuyansu a kan lokaci domin tabbatar da ci gaban bangaren ilimi a jihar.

'Gwamnatin Kano bata da niyan cin zarafin kowa', hadimin gwamna

Hadimin gwamnan ya kuma bukaci jama'a da kada su dauki wannan kokari da ake na dawo da tsarin kula da makarantu masu zaman kansu a matsayin barazana, a cewarsa, gwamnatin bata da niyar cin zarafin kowa.

Har ila yau, gwamnatin jihar ta bayyana kudirinta na daukar matakan da suka dace kan duk wata makaranta mai zaman kanta da aka samu ta keta wannan ka’ida.

Kara karanta wannan

Daga karshe: Malaman Izala sun dira Nijar don neman hanyar sulhu a batun juyin mulki

Ya kuma bayyana cewa an samar da wata manhaja da za ta magance duk wata matsala daga bangaren gwamnati, masu makarantu, iyaye da ma masu neman aiki a makarantun, inda ya bai wa iyaye tabbacin kare muradunsu da yaransu.

A nasa bangaren, shugaban kungiyar mamallaka makarantu masu zaman kansu na kasa reshen Jihar Kano, Alhaji Muhammad Malam Adamu, ya yaba da wannan mataki na gwamnatin domin a cewarsa hakan zai kara bunkasa harkar ilimi a jihar.

Gwamnatin Kano ta soke lasisin yan Kannywood gaba daya

A wani labari makarancin wannan, mun kawo a baya cewa gwamnatin jihar Kano ta soke lasisin gaba daya yan masana'antar shirya fina-finan Hausa ta Kannywood.

Kamar yadda shugaban kungiyar tantance fina-finai na jihar, Abba El-Mustapha ya bayyana, an dauki matakin ne domin tsaftace masana'antar da kuma cire baragurbi a cikinsu.

Asali: Legit.ng

Authors:
Aisha Musa avatar

Aisha Musa (Hausa writer) Aisha Musa 'yar jarida ce wacce ta kwashe shekaru biyar tana aikin gogewa a harkar yada labarai. Ta kammala karatun ta a Jami'ar Ibrahim Badamasi Babangida (IBB Lapai) a shekarar 2014 tare da digirin farko a fannin Tarihi. Aisha Editan Hausa ce wacce ke amfani da kwarewa da kwazonta don karfafawa wasu gwiwar yin aiki tukuru don cimma nasara. Ta karbi lambar yabo na gwarzuwar shekarar 2021 a bangaren Hausa na Legit. Za ku iya aika mata sakonnin imel ta adireshinta aisha.musa@corp.legit.ng

Online view pixel