Jerin Shugabannin da Suka Shafe Shekaru Sama da 30 Suna Mulki a Kasashensu a Nahiyar Afrika

Jerin Shugabannin da Suka Shafe Shekaru Sama da 30 Suna Mulki a Kasashensu a Nahiyar Afrika

A Afirka, wasu shugabannin sun shafe sama da shekaru 30 suna mulki, wasu shugabannin kasar suna rike da madafun iko duk da kuwa sun tsufa kuma ya kamata su huta su ba wani.

DUBA NAN: Bibiyi shafin Legit.ng Hausa a kafar TikTok. Kada ka bari bidiyo mai daukar hankali ya wuce ka!

Wadannan shugabanin da suka dade suna kan karagar mulki sukan ce har yanzu suna mulki ne saboda muradin ‘yan kasarsu.

A yau, wannan cikakken rahoto ya tattaro jerin sunayen shugabannin Afirka da suka fi dadewa kan karagar mulki a halin yanzu.

Yadda ake mulkan wasu kasashen Afrika
Shugabannin wasu kasashen Afrika | Hotuna: GettyImages
Asali: Getty Images

Ga jerin kasashen da shugabanninsu kamar haka:

1. Faure Gnassingbe, shugaban kasar Togo

Tun shekara ta 2005 Faure Gnassingbe ne ke kan shugabancin kasar Togo, kuma kafin shi mahaifinsa Gnassingbe Eyadéma ne ya yi mulki tun shekara ta 1967.

DUBA: Bibiyemu a Instagram don samun labarai masu muhimmanci kai tsaye cikin manhajar

Kara karanta wannan

Mun fi karfinku: Jigon APC ya gargadi sojojin Mali, Nijar da suke barazanar taran na Najeriya

Tun lokacin da ya karbi ragamar shugabancin Jamhuriyar Togo, Shugaba Faure Gnassingbe ya yi aiki don samar da sulhu na kasa da kuma yanayin siyasa cikin lumana.

A karkashin jagorancinsa, tattalin arzikin Togo na ta habaka kuma kasar ta shiga wani yanayi na zamanantarwa duk saboda jajircewarsa.

Gnassingbe na Togo a yanzu haka yana kan karagar mulki ne karo na 4 bayan mahaifinsa ya shafe shekaru 38 yana mulki.

2. Ali Bongo, shugaban kasar Gabon

Bongo mutum ne mai fuskoki da dama wanda a yanzu ke mulkin Gabon mai arzikin man fetur a matsayin wani yanki na gadonsa.

Ya kama mulki ne bayan rasuwar mahaifinsa, inda a yanzu yake rike da mukamin da ahalinsa ke rike dashi sama da shekaru 50 kenan.

3. Paul Biya, shugaban jamhuriyar Kamaru

Paul Biya ne shugaban jamhuriyar Kamaru, wanda ya shafe shekaru 41 a matsayin shugaban farar hula a kasar.

Biya ya kasance firayim minista na tsawon shekaru bakwai kafin ya zama shugaban kasa daga bisani.

Kara karanta wannan

Shikenan: Sanatocin Najeriya sun yi maganar karshe kan batun tura sojojin Najeriya su yaki na Nijar

An haifi Biya ne a ranar 13 ga Fabrairu, 1933 a Mvomeka'a, yankin Meyomessala. Shi da ne ga Etienne Mvondo Assam da Anastasie Eyenga Elle.

Shi ne shugaban Kamaru na biyu a tarihi. Biya ya hau kan karagar mulki ne a ranar 6 ga watan Nuwamban 1982 bayan shugaba Ahmadou Ahidjo ya yi murabus a ranar 4 ga watan Nuwamba.

4. Teodoro Obiang Nguema Mbasogo, shugaban Equatorial Guinea

Theodore Obiang na Equatorial Guinea ya kwashe shekaru 44 yana shugabancin farar hula inda ya maye gurbin kawunsa.

Shugaban da aka haifa a ranar 5 ga Yuni, 1942, Teodoro Obiang Nguema, ya tsallake rijiya da baya a yunkurin juyin mulki da dama, ya samu mulkin kasar ta Afirka ta Yamma mai arzikin man fetur ne a 1979 bayan da sojoji suka ui juyin mulki.

Bayan samun mukami daga magabacinsa kuma kawunsa, Francisco Macias Nguema, ya yi wasu gyare-gyare, amma ya ci gaba da rike cikakken ikon Nguema kan al'ummar kasar.

Kara karanta wannan

'Yan Daba Sun Afka Wa Manyan APC, Sun Barnata Kayayyaki Na Miliyoyi, Bayanai Sun Fito

5. Isma'il Omar Guelleh, shugaban Djibouti

Omar Guelleh shi ne shugaban jamhuriyar Djibouti, wanda ya yi shugabancin farar hula tsawon shekaru 24 da suka gabata zuwa yanzu bayan maye gurbin kawunsa.

A watan Afrilun 2021, an sake zabensa shugaba Djibouti Ismail Omar Guelleh a wa'adi na 5 da sama da kashi 98% na kuri'un da aka kada.

Ya yi mulki ne tun a shekarar 1999 lokacin da ya karbi mulki daga hannun kawunsa, shugaban kasar Djibouti na farko kuma firaministan kasar, Hassan Gouled Aptidon wanda ya yi mulki daga 1977 zuwa 1999.

Jigon APC ya gargadi sojojin Mali, Nijar da suke barazanar taran na Najeriya

A wani labarin, tsohon ministan sufurin jiragen sama, Femi Fani-Kayode, ya yi wani kakkausan gargadi ga shugabannin mulkin soja a Nijar, Mali da Burkina Faso kan abin da ya bayyana a matsayin barazana ga Najeriya.

Jigon na jam’iyyar APC mai mulki ya bukaci shugabannin da suka yi juyin mulki da kada su tunzura Najeriya a yanayi irin wannan.

Kara karanta wannan

‘Yan Kasuwa Sun Nuna Abin da Zai Jawo Man Fetur Ya Sauko Daga N620 a Farat Daya

Bayan juyin mulkin da aka yi a jamhuriyar Nijar a baya-bayan nan da ya hambarar da shugaban kasar Mohamed Bazoum, ECOWAS, ta ba gwamnatin mulkin soji a Nijar wa'adin kwanaki bakwai da ta dawo da hambararren shugaban.

Asali: Legit.ng

Authors:
Salisu Ibrahim avatar

Salisu Ibrahim (Head of Hausa Desk) Salisu holds BSc in IT (IOU, 2021) and is AfricaCheck's ambassador. He brings over five years of experience in writing, publishing and management. Trained by prestigious newspapers like Reuters, AFP, and Solutions Journalism Network, he curates news stories for the Hausa-speaking audience. He rose from Hausa Editor to Head of Desk at Legit. His commitment to excellence has earned him recognition, including the 2021 Best Hausa Editor award and the Legit Fearless Team Player of the Year 2023.