Lambar Ministan Buhari Ta Fito, Gwamnatin Tinubu Za Ta Bincike Shi Kan Abubuwa 5
- Gwamnatin Najeriya za tayi bincike a kan Abubakar Malami wanda ya rike AGF daga 2015 zuwa 2023
- Tsohon Ministan zai amsa tambaya a kan kudin da gwamnatin tarayya ta biya lauyoyi da kamfanoni
- Abubakar Malami SAN yana cikin Ministocin da su ke da karfi a mulkin Muhammadu Buhari
DUBA NAN: Bibiyi shafin Legit.ng Hausa a kafar TikTok. Kada ka bari bidiyo mai daukar hankali ya wuce ka!
Abuja- Akwai wasu ciniki da yarjejeniya da aka shiga a lokacin da Muhammadu Buhari yake mulki da su ka jefa Abubakar Malami a matsala.
Wani rahoto na musamman da aka samu daga The Cable ya nuna cewa akwai zargin badakala akalla biyar da ke wuyan Abubakar Malami SAN.
Daga ciki akwai Dala miliyan $496 da kamfanin Global Steel Holdings Ltd (GSHL) ya biya gwamnatin tarayya kan kwangilar kamfanin Ajaokuta.

Source: Getty Images
Binciken EFCC da Paris Club
Tsohon Ministan shari’an kasar zai amsa tambayoyin inda aka kai kadarori da sauran kudin da EFCC ta karbe daga hannun marasa gaskiya.
DUBA: Bibiyemu a Instagram don samun labarai masu muhimmanci kai tsaye cikin manhajar
Baya ga haka, za a ji gaskiyar dalilin biyan Dala miliyan $419 ga wasu kwararru daga kudin Paris Club, a yayin da Malami yake rike da ofishin AGF.
Binciken ya tabo Dala miliyan $200 da gwamnatin Najeriya ta biya kamfanin Sunrise Power sakamakon sabanin da aka samu a aikin wutan Mambilla.
Ana zargin an biya kudin shari’a sau biyu domin karbo Dala miliyan $321 da aka karbe daga hannun Marigayi Janar Sani Abacha a Switzerland.
A lokacin Kayode Fayemi yana Minista, ya ce an shawo kan matsalolin kamfanin Ajaokuta, daga baya aka ji Malami ya ce za a biya $496m ga GSHL.
Rahoton ya ce ana zargin Malami ya ba EFCC ta ofishin Ladidi Mohammed umarnin yin gwanjon wasu kadarori da hukumar ta yi nasarar karbewa a kasar.
Wajen aikin wutan Mambila, tsohon Lauyan da Saleh Mamman su ka sa hannu aka biya kamfanin SPTCL dalolin kudi domin su janye kararsu a kotu.
A kokarin dawo da kudin Abacha daga Switzerland, gwamnatin tarayya ta biya $17m ga wasu lauyoyi, wannan yana cikin dalilin binciken tsohon Minista.
Bashin Paris Club ya jawo rikici
A baya an ji labari NGF ta sa kafar wando daya da Abubakar Malami kan bashin Paris Club saboda ya ce za a biya kudi ga wasu da sunan kudin aiki.
Malami ya zaftare fiye da N170bn daga asusun jihohi da kananan hukumomi a 2022, ya ce zai biya wasu da su ka taimaka har aka iya dawo da dalolin.
Asali: Legit.ng

