'Yan Bindiga A Zamfara Sun Yi Barazanar Auren 'Yan Mata 4 Da Ke Hannunsu

'Yan Bindiga A Zamfara Sun Yi Barazanar Auren 'Yan Mata 4 Da Ke Hannunsu

  • Masu garkuwa da mutane sun yi barazanar auren wasu 'yan mata hudu nan da mako daya idan ba a biya kudi ba
  • An kama 'yan matan ne akan hanyar Birnin Magaji zuwa Kaura Namoda watanni shida da suka wuce
  • Iyalan 'yan matan su hudu sun roki gwamnati da al'umma da su kawo musu dauki don ceto yaran

Jihar Zamfara - 'Yan bindiga sun yi barazanar auren 'yan matan da suka yi garkuwa da su idan iyayensu suka gagara biyan kudin fansa.

'Yan bindigan sun sace 'yan matan ne su hudu akan hanyar Birnin Magaji zuwa Kaura Namoda da ya hada da wata dalibar Kwalejin Kimiyya da Adabi ta jihar inda suka bukaci kudin fansa Naira miliyan 12.

'Yan Bindiga A Zamfara Sun Yi Barazanar Auren 'Yan Mata 4 Da Suka Sace
'Yan Bindiga Sun Addabi Yankuna Da Dama A Jihar Zamfara Musamman Mutanen Karkara. Hoto: Daily Post.
Asali: Facebook

'Yan matan da aka kaman watanni shida da suka wuce sun bayyana yadda 'yan bindigan suke musu barazanar aure a wani faifan bidiyo, cewar gidan talabijin na Channels.

Kara karanta wannan

'Yan Bindiga Sun Hallaka Wani Matashi A Kokarin Sace Yaro A Katsina, Ba Su Yi Nasarar Sace Yaron ba

Matan sun hada da Ummukhair da Aisha Yahaya da Jemila Yahaya sai kuma Ummu Sani.

DUBA: Shigo shafin Legit.ng na manhajar Legit.ng na Telegram! Kada ka bari komai ya wuce ka

Sun ce tsagerun sun ba wa iyayensu mako daya su kawo kudin fansa ko kuma su aure su gaba daya, cewar Ripples.

A cewarsu:

"Muna rokonku iyayen mu don girman Allah, muna cikin wani hali, don Allah ku nemo kudi don samar mana 'yanci.
"Gwamnatin Matawalle ta gaza yin wani abu, wannan watan mu na shida kenan, muna rokon Dauda Lawal ya yi wani abu."

Daya daga cikin 'yan uwan matan da aka kaman, Aminu Yahaya ya bayyana cewa su shida aka kama amma an saki biyu bayan biyan kudin fansa na N6m, Daily Post ta tattaro.

"Ni na kai kudin fansa N6m kafin suka saki 'yan mata biyu.
"Yanzu sun bamu mako daya idan ba mu kawo N12m ba za su auri kannenmu."

Kara karanta wannan

'Yan Sanda A Kano Sun Bazama Neman Makerar Da Ke Ingiza Ta'addanci A Jihar, Sun Yi Gargadi

Ya roki gwamnati da kuma al'umma da su kawo musu dauki.

Rundunar Soji Sun Fatattaki 'Yan Bindiga Da Dama a Jihar Zamfara

A wani labarin, rundunar soji sun hallaka wasu 'yan bindiga da dama a jihar Zamfara.

Rahotanni sun tabbatar cewa sojojin sun hallaka 'yan bindigan bayan kai samame maboyar 'yan ta'addan.

Ƙauyukan da sojojin suka kai hari akwai Mutuwa da Guda Tudu da Kawar da kuma Dan Kare da ke jihohin Zamfara da Sokoto.

Asali: Legit.ng

Authors:
Abdullahi Abubakar avatar

Abdullahi Abubakar (Hausa editor) Marubuci kuma kwararren ɗan jaridan da ya shafe shekaru 3 yana rubutu a fannin siyasa da harkokin yau da kullum. Ya kammala digirin farko a jami'ar Maiduguri. Ya samu horon aikin jarida a Reuters da AFP, ya sha halartar tarukan karawa juna sani game da bincike da adabi. Tuntube shi a abdullahi.abubakar@corp.legit.ng.