Daga Karshe Majalisar Dattawa Tayi Magana Akan Wadanda Tinubu Zai Nada Su Zama Ministocinsa

Daga Karshe Majalisar Dattawa Tayi Magana Akan Wadanda Tinubu Zai Nada Su Zama Ministocinsa

  • Jinkirin da shugaba Bola Tinubu ya yi na aika sunayen ministocinsa zuwa majalisar dattawa zai tilastawa majalisar dakatar da hutun da take yi na shekara-shekara
  • A ranar 27 ga watan Mayu ne ake sa ran majalisar dattijai za ta fara hutun ta, sai dai wata majiya daga majalisar ta bayyana cewa ana sa ran ganin jerin ministocin daga farkon mako mai zuwa
  • Sai dai kakakin majalisar dattawan ya ce ba a bayyana ranar hutun ba, kuma babu bukatar a yi muhawara kan karin wa'adin tafiya hutun

DUBA NAN: Bibiyi shafin Legit.ng Hausa a kafar TikTok. Kada ka bari bidiyo mai daukar hankali ya wuce ka!

FCT, Abuja - Majalisar dattawa za ta dakatar da hutun da za ta yi na shekara saboda an ce tana sa ran ganin ministocin da shugaba Bola Tinubu ya nada domin tantance su.

Kamar yadda shafin jaridar The Nation ya ruwaito, 'yan majalisar na jiran jerin sunayen ne daga fadar shugaban kasa a farkon mako mai zuwa.

Kara karanta wannan

Tallafin Tinubu: “Rabon N8,000 Duk Yaudara Ce”, Gwamnan Kaduna Ya Fadi Dalili

Wani babban jami’in majalisar dattawan ya bayyana cewa ana sa ran majalisar ta fara hutun shekara-shekara, wanda ake sa ran zai fara daga ranar 27 ga watan Yuli zuwa Satumba.

Jerin Ministocin Tinubu na duhu har yanzu
Shugaban majalisa Akpabio da Tinubu shugaban Najeriya | Hoto: Bola Ahmed Tinubu
Asali: Facebook

Dalilin da ya sa Majalisar Dattawa ta dakatar da hutun shekara

Sai dai, yanzu an ce majalisa a shirye take ta rika zama a kowace rana domin tabbatar da an tantance wadanda Tinubu zai nada, koda kuwa hakan na nufin za a daga lokacin tafiya hutun da mako guda.

DUBA: Bibiyemu a Instagram don samun labarai masu muhimmanci kai tsaye cikin manhajar

Shugaban kwamitin majalisar dattawa kan harkokin yada labarai, Yemi Adaramodu, ya ce majalisar na da karin lokaci don duba bukatar shugaban kasa kafin a tafi hutu.

A cewarsa, har yanzu ba a bayyana ranar da za a fara hutun shekaran ba. Don haka, tambayar canjin lokacin ma bai taso ba.

Majalisar dattawa za ta duba jerin sunayen ministocin shugaba Tinubu

Kara karanta wannan

Daga Karshe, Majalisar Dattawa Ta Yi Magana Kan Sunayen Ministocin Shugaba Bola Tinubu

Yace:

"Har yanzu akwai isasshen lokaci na gudanar da tantance sunayen ministocin."

Adaramodu ya ci gaba da cewa, majalisar dokokin kasar za ta yi abin da ya dace kuma ‘yan Najeriya ba za su ji kunya ba.

A baya dai an ruwaito cewa shugaba Tinubu ya mika sunayen wadanda aka nada a matsayin ministoci ga majalisar dokokin kasar.

An kuma bayyana cewa shugaban ya aika da jerin sunayen ga hukumar tsaro ta farin kaya (DSS) da kuma hukumar yaki da masu yi wa tattalin arzikin kasa zagon kasa (EFCC) domin tantancewa.

Jerin mutane 50 da Bola Tinubu ya fito da su a siyasa har Duniya ta san da zamansu yau

A wani jeri da yake yawo a kafafen sada zumunta, Legit.ng Hausa ta tattaro sunayen wasu da-dama daga cikin wadanda za a kira yaran Bola Tinubu.

A baya, mun tuntubi Hadimin Gwamnan jihar Legas, Jibril Gawat domin jin yadda lamarin yake.

Kara karanta wannan

Kowa Zai Samu: Gwamnati Ta Bayyana Yadda Rabon N8000 Na Tinubu Zai Wakana

Jibril Gawat ya shaida mana cewa gwanin na su ya kafa mutanen da ba za su kirgu ba, ya kuma yi alkawarin zai tattaro mana sunayen wasu daga cikinsu.

Asali: Legit.ng

Authors:
Salisu Ibrahim avatar

Salisu Ibrahim (Head of Hausa Desk) Salisu holds BSc in IT (IOU, 2021) and is AfricaCheck's ambassador. He brings over five years of experience in writing, publishing and management. Trained by prestigious newspapers like Reuters, AFP, and Solutions Journalism Network, he curates news stories for the Hausa-speaking audience. He rose from Hausa Editor to Head of Desk at Legit. His commitment to excellence has earned him recognition, including the 2021 Best Hausa Editor award and the Legit Fearless Team Player of the Year 2023.