Bayan Tafka Asara A 2022, Elon Musk Ya Dawo Matsayi Na 1 Da $250bn, Zuckerberg Ya Fado, Dangote Ya Kara Sama

Bayan Tafka Asara A 2022, Elon Musk Ya Dawo Matsayi Na 1 Da $250bn, Zuckerberg Ya Fado, Dangote Ya Kara Sama

  • Aliko Dangote ya ci ribar akalla dala miliyan 272 a rana daya inda ya kwace matsayin shi na farko a Nahiyar Afirka da $16.4bn
  • Elon Musk ya ci kazamin riba a cikin mako daya inda ya samu dala biliyan 11, yayin da kudinsa ya kai $250bn
  • Mamallakin Facebook, Mark Zuckerberg ya tafka asara yayin da ya dawo na tara a jerin masu kudin duniya

DUBA NAN: Bibiyi shafin Legit.ng Hausa a kafar TikTok. Kada ka bari bidiyo mai daukar hankali ya wuce ka!

Mai kamfanin Twitter, Elon Musk ya dawo matsayinsa na wanda ya fi kowa kudi a duniya bayan asarar $200bn a shekara daya.

Musk ya rike matsayin nasa ne bayan adadin kudin da ya ke da shi ya kai har $250bn a jerin masu kudin duniya da mujallar Forbes ta sake.

Elon Musk Ya Dawo Matsayin Na 1 Da $250bn, Zuckerberg Ya Yi Asara, Dangote Ya Yi Sama
Mujallar Forbes Ta Bayyana Elon Musk A Matsayin Na 1 A Duniya Bayan Tafka Asara A 2022, Zuckerberg Ya Yi Asarar $1bn, Yayin Da Dangote Ya Farfado. Hoto: Elon Musk, Aliko Dangote and Mark Zuckerberg.
Asali: Getty Images

Kamar yadda Bloomberg ya tattaro. Elon Musk ya samu $11bn a cikin kwanaki biyar kacal.

Kara karanta wannan

Yanzu nan: Shugaban APC Ya Hakura da Rikon Jam’iyya, Ya Sauka Daga Kujerarsa

Musk ya yi sama, yayin da Zuckerberg ya tafka mummunar asara

Har ila yau, abokin hamayyarsa Mark Zuckerberg ya fado a matsayi na tara a jerin wadanda suka fi kowa kudi a duniya bayan asarar $1bn.

LURA: Shin kana son bamu labari da tattaunawa da marubutanmu? Tuntubemu a info@corp.legit.ng

Zuckerberg ya sauko kasan ne bayan tafka asara da ya yi a wannan Juma’a 14 ga watan Yuli 2023, cewar Legit.ng.

Aliko Dangote, wanda ya fi kowa kudi a Nahiyar Afirka ya kara samun daukaka inda kudinsa ya kai $16.4 bayan samun ribar $272m a ranar Juma’a 14 ga watan Yuli.

Dangote ya farfado bayan sauye-sauyen hada-hadar kudade

Dangote, wanda ya yi asarar kusan $3bn a cikin wata biyu bayan sauye-sauye da aka samu a kasuwar hada-hadar kudade ya fara dawowa hayyacinsa.

Dalilin asarar, Dangote ya yi kasa a cikin wadanda suka fi kowa kudi daga 76 zuwa 122 yayin da ya kuma rasa matsayin shi na wanda ya fi kudi a Afirka.

Kara karanta wannan

Mataimakin Kakakin Majalisar Wakilai Ya Bayyana Yadda Wani Yankin Najeriya Ya Yi Asarar N4trn Cikin Shekara Biyu Saboda Dalili 1 Rak

Daga bisani Dangote bayan ribar da ya samu ya dawo matsayin shi na wanda ya fi kudi a Nahiyar Afirka inda ya sake doke dan kasar Afirka ta Kudu, Johann Rupert a farkon watan Yuni.

Dangote Ya Rasa Matsayin Wanda Ya Fi Arziki A Afirka, Dan Afirka Ta Kudu Ya Doke Shi

A wani labarin, shahararren dan kasuwa kuma mai kudin Najeriya, Aliko Dangote ya rasa matsayinsa na wanda yafi kowa kudi a Afirka.

Aliko Dangote ya tafka asarar $3.4bn bayan faduwar dala a kasar Najeriya da sauran sauye-sauye.

Dan Afirka ta Kudu, Johann Rupert shi ya maye gurbin Dangote a matakin farko a jerin masu kudin.

Asali: Legit.ng

Authors:
Abdullahi Abubakar avatar

Abdullahi Abubakar (Hausa editor) Marubuci kuma kwararren ɗan jaridan da ya shafe shekaru 3 yana rubutu a fannin siyasa da harkokin yau da kullum. Ya kammala digirin farko a jami'ar Maiduguri. Ya samu horon aikin jarida a Reuters da AFP, ya sha halartar tarukan karawa juna sani game da bincike da adabi. Tuntube shi a abdullahi.abubakar@corp.legit.ng.