Malam Daurawa Ya Fara Shirin Daura Auren Mutum 1,000 a Jihar Kano

Malam Daurawa Ya Fara Shirin Daura Auren Mutum 1,000 a Jihar Kano

  • Shugaban hukumar Hisbah da gwamna Abba Kabir Yusuf ya naɗa a Kano ya shiga Ofis ranar Laraba, 12 ga watan Yuni, 2023
  • Sheikh Aminu Ibrahim Daurawa ya ce tuni suka fara shirye-shiryen ɗaura aure 1,000 a faɗin kananan hukumomi 44
  • Ya ce hukumar Hisbah ba zata yi ƙasa a guiwa ba wajen ganin ta tsaftace Kano daga kowane irin aikin rashin ɗa'a

Kano state - Sabon Kwamandan rundunar 'yan sandan Musulunci watau Hisbah ta jihar Kano, Sheikh Aminu Ibrahim Daura, ya kama aiki gadan-gaban.

Sheikh Daurawa ya ce tuni shirye-shirye suka yi nisa na aurar da 'yan mata da zawarawa 1,000 karkashin rundunar Hisbah a faɗin jihar Kano.

Kwamandan hukumar Hisbah, Sheikh Aminu Ibrahim Daurawa.
Malam Daurawa Ya Fara Shirin Daura Auren Mutum 1,000 a Jihar Kano Hoto: Sheikh Aminu Ibrahim Daurawa
Asali: Facebook

Kwamandan ya bayyana haka ne a jawabinsa na farko bayan shiga Ofis wanda ya ɗora a shafinsa na Facebook ranar Laraba, 12 ga watan Yuli.

Kara karanta wannan

Shugaban Tinubu Ya Ayyana Ta Ɓaci Kan Batun Samar da Abinci a Najeriya, Ya Bada Sabon Umarni

Idan baku manta ba Daurawa ya yi aiki a matsayin kwamandan Hisbah a lokacin mulkin Rabiu Musa Kwankwaso da Abdullahi Ganduje.

Shin kana da labarin da ka/ki ke son an wallafa ma ka/ki? Ka tuntubemu a info@corp.legit.ng!

Bayan Daurawa ya bar muƙamin a shekarun baya, a halin yanzu gwamna Abba Kabir Yusuf ya sake dawo da Shehin Malamin, ya naɗa shi kwamandan Hisbah a karo na uku.

Zamu raba Fam kowace karamar hukuma - Daurawa

Da yake jawabi jim kaɗan bayan shiga Ofis, Sheikh Aminu Daurawa ya bayyana cewa sabon gwamna, Abba Gida-Gida dagaske yake wajen inganta walwalar mutanen Kano.

Game da ƙulla aure 1,000 kuwa, Daurawa ya ce sun kafa kwamitoci daban-daban domin tabbatar da an samu nasarar haɗa ɗaruruwan ma'aurata a faɗin jihar Kano.

Ya kuma kara da cewa hukumar Hisbah zata raba Fom guda 20 ga kowace ƙaramar hukumar a cikin ƙananan hukumomi 44 da ke faɗin jihar.

Kara karanta wannan

Rusau: Abba Gida Gida Ya Ce Ko Kaɗan Bai Yi Nadama Ba Kan Abinda Ya Ke Yi A Kano

Ya ce:

"Zamu ba kowane kwamandan ƙaramar hukuma Fam 20, ya tantance mutanen da suka cike domin ɗaura musu aure."

Wace hanya za a samu kuɗin aikata wannan kyakkyawan aiki?

Sheikh Daurawa ya yi bayanin cewa kofar hukumar Hisbah a buɗe take ga duk wanda ke da niyyar tallafawa wajen ganin an cimma nasarar ɗaura aure 1000.

"Hukumar Hisbah ta ba zata yi ƙasa a guiwa ba a kokarinta na tsaftace jihar Kano daga aikata munanan ɗabi'u," inji Malam Daurawa.

Gwamnan Jigawa Umar Namadi Ya Rantsar da Sabbin Kwamishinoni 16

A wani labarin kuma Gwamna Umar Namadi na jihar Jigawa ya rantsar da sabbin kwamishinoni 16 a gidan gwamnatinsa da ke Dutse.

Gwamna Namadi ya buƙaci kwamoshinoni su yi aiki bisa tsoron Allah, gaskiya da riƙon amanar al'umma da kuma sauke haƙƙi.

Asali: Legit.ng

Authors:
Ahmad Yusuf avatar

Ahmad Yusuf (Hausa editor) Ahmad Yusuf ma'aikacin jaridar Legit.ng sashin Hausa ya fara aiki a 2021, ya kware wajen kawo labarai da rahotanni da suka shafi siyasa da al'amuran yau da kullum. Matashin ɗan jaridar ya koyi Lissafi a digirinsa na farko a Jami'ar Kimiyya da Fasaha da ke Wudil, Kano (KUST) ya kuma samu shaidar kwarewa a fannin aikin jaridar zamani daga Reuters a 2022. Kafin fara aiki da Legit Ahmad ya yi aiki da jaridu da dama na turanci da Hausa tun 2012. Mail: ahmad.yusuf@corp.legit.ng 07032379262