An Ga Watan Dhul Hijjah a Saudiyya: Muhimman Ranakun da Ya Kamata Duk Musulmi Ya Kiyaye

An Ga Watan Dhul Hijjah a Saudiyya: Muhimman Ranakun da Ya Kamata Duk Musulmi Ya Kiyaye

  • Kasar Saudiyya ta sanar da ganin jinjirin watan Dhull Hijjah na wannan shekarar, za a fara aikin Hajjin bana
  • Tuni Musulmai daga sassan duniya suka fara tafiyar ziyara zuwa kasar domin gudanar da aikin na Hajji
  • Ya zuwa yanzu, jirage daga Najeriya sun sauka Saudiyya, duk da an samu tsaiko a tashin jiragen wasu jihohi

Kasar Saudiyya - Kotun kolin kasar Saudiyya ya sanar da ganin jinjirin watan Dhul Hijjah da ake gudanar da ayyuka Hajji, Arab News ta ruwaito.

Bana ma bata sauya zane ba, za a fara gudanar da shirye-shiryen ayyukan Hajjin bana daga ranar 1 ga watan Dhul Hijjah, wanda ya yi daidai da ranar 19 ga watan Yuni.

Hakan na nufin cewa, a ranar 26 ga watan Yuni da ya yi daidai da 8 ga watan Dhul Hijjah ne za a fara gudanar da aikin Hajji, wanda dukkan Musulmin da suka samu dama za su fara.

Kara karanta wannan

Babban Sallah: Sarkin Musulmi Ya Fadi Ranar Da Ya Kamata a Fara Duba Jinjirin Watan Dhul-Hijjah

Yadda aikin hajjin bana zai kasance
An ga watan Dhul Hijjah a kasar Saudiyya | Hoto: @HaramainInf
Asali: Twitter

Hakazalika, a ranar 27 ga watan Yuni, wanda ya yi daidai da 9 ga watan Dhul Hijjah za a yi tsayuwar Arafah, kamar yadda addinin Islama ya tanada.

LURA: Shin kana son bamu labari da tattaunawa da marubutanmu? Tuntubemu a info@corp.legit.ng

Musulmin da ba su samu damar zuwa aikin Hajjin bana ba, za su yi bikin Sallar Idi ne a ranar Laraba 28 ga watan Yuni da ya yi daidai da 10 ga watan na Dhull Hijjah.

Aikin Hajji ga Musulmi a duniya

Kamar yadda addinin Islama ya tanada, ya wajaba a kan dukkan Musulmin da ya samu damar zuwa ziyarar Hajji ya gudanar da ibadar sau daya a rayuwarsa.

Aikin hajji, na daya daga cikin rukunan addinin Islama guda biyar wadanda suka hada da; Shahada, Sallah, Azumi, Zakkah sai na biyar din kuwa Hajji.

A halin da ake ciki, Musulmai daga kasashen duniya sun fara dura a kasar Saudiyya domin gudanar da wannan ibada mai muhimmanci.

Kara karanta wannan

Sabon Gwamna Zai Ba Mazauna Garuruwa Makamai Domin Yakar ‘Yan Bindiga a Arewa

Yadda Alhazan Najeriya Mata 75 Suka kare a Asibitocin Makkah da Madina

Hukumar kula da alhazai ta kasa (NAHCON) ta bayyana cewa kawo yanzu an kwantar da maniyyata mata 75 masu ɗauke da juna biyu a asibitocin Makkah da Madina.

Jaridar Punch ta rahoto ce an garzaya da maniyyatan masu ciki Asibiti ne domin kula da lafiyarsu sakamakon abinda su ke dauke da shi kuma ga aikin Hajji.

NAHCON ta ce mafi yawan maniyyata sun sa kafa sun shure shawarwari da kuma wayar da kan da aka musu kan cewa duk mace mai juna biyu ta haƙura da tafiya aikin Hajjin bana.

Asali: Legit.ng

Authors:
Salisu Ibrahim avatar

Salisu Ibrahim (Head of Hausa Desk) Salisu holds BSc in IT (IOU, 2021) and is AfricaCheck's ambassador. He brings over five years of experience in writing, publishing and management. Trained by prestigious newspapers like Reuters, AFP, and Solutions Journalism Network, he curates news stories for the Hausa-speaking audience. He rose from Hausa Editor to Head of Desk at Legit. His commitment to excellence has earned him recognition, including the 2021 Best Hausa Editor award and the Legit Fearless Team Player of the Year 2023.