Binciken Kwakwaf: Shugaban Kasa Bola Tinubu Bai Nada Ministoci 27 Ba

Binciken Kwakwaf: Shugaban Kasa Bola Tinubu Bai Nada Ministoci 27 Ba

  • Jerin sunayen sabbin nade-nade da wasu sabbin ma'aikatu da shugaban kasa Bola Tinubu ya samar na ta yawo a Facebook
  • Sai dai kuma, rahoton wani binciken kwakwaf ya gano jerin sunayen na bogi ne, yana mai cewa babu wata sanarwa a hukumance daga fadar shugaban kasa
  • Jerin sunayen ya yi ikirarin cewa an nada Femi Falana a matsayin ministan shari'a, Pat Utomi a matsayin minidtan ci gaba da tsare-tsaren kasa

An gano cewa jerin sunayen sabbin nade-nade 27 da wasu sabbin ma'aikatu da ake zargin shugaban kasa Bola Tinubu ya samar kuma suka karade Facebook na bogi ne.

Kamar yadda Africa Check, wani dandamalin binciken kwakwaf ya rahoto, ana ta yada jerin sunayen mutanen 27 wanda aka tabbatar da karya ne, a shafukan Facebook, tare da ikirarin cewa shugaban kasa Tinubu ya soke wasu kujerun ministoci.

Kara karanta wannan

Sabon Gwamnan CBN: Tsohon Gwamna, Masu Bankuna Da Wasu Kwararru Da Ke Sa Ran Gaje Kujerar Emefiele

Shugaban kasa Bola Tinubu da wasu shahararrun yan Najeriya
Binciken Kwakwaf: Shugaban Kasa Bola Tinubu Bai Nada Ministoci 27 Ba Hoto: Asiwaju Bola Ahmed Tinubu/Pat Utomi/ Pastor Tunde Bakare/Inibehe Effiong
Asali: Facebook

A bisa ga wallafar ta Facebook, an nada shahararren faston Najeriya, Tunde Bakare a matsayin mai ba Tinubu shawara ta musamman yayin da aka nada Pat Utomi, masanin tattalin arziki kuma jigon jam'iyyar Labour Party a matsayin ministan ci gaba da tsare-tsaren kasa.

Rahoton ya kuma ce an nada mai rajin kare hakkin dan adam, Femi Falana a matsayin ministan shari'a.

LURA: Shin kana son bamu labari da tattaunawa da marubutanmu? Tuntubemu a info@corp.legit.ng

Ku yi watsi da sunayen, Utomi ga yan Najeriya

Daya daga cikin sunayen da ke jerin takardar, Utomi, ya karyata ikirarin cewa an nada shi mukamin minista a gwamnatin Tinubu. Utomi ya bukaci yan Najeriya da su yi watsi da sunayen, jaridar Punch ta rahoto.

Tsarin nada ministoci

Ku tuna cewa wani kudiri da tsohon shugaban kasa Muhammadu Buhari ya aiwatar, ya yi umurnin cewa sabuwar gwamnari ta nada ministoci cikin kwanaki 60.

Kara karanta wannan

Ranar Damokradiyya: Shehu Sani Ya Saki Jerin Sunayen Yan Arewa Da Suka Yi Fafutukar June 12

Sannan sai a aika sunayen don yan majalisa su tantance sunayen ministocin da aka aika a majalisar dokokin tarayya.

Akwai yiwuwar a watsa shirye-shiryen tabbatar da sunayen a majalisar dokoki kai tsaye kamar yadda aka saba yi a baya.

Babu wani abu mai kama da wannan da ya faru kuma babu kafar watsa labarai da ta kawo rahoton irin haka tun da shugaban kasa Tinubu ya hau karagar mulki a ranar 29 ga watan Mayu.

Shugaban kasa Bola Tinubu ya rage alawus din yan NYSC? Gaskiya ta bayyana

A wani labarin, mun ji cewa an gano cewa hotuna da dama da masu amfani da dandalin WhatApp suka daura a shafukansu na ikirarin cewa Shugaban kasa Bola Tinubu na shirin rage alawus din da ake ba yan bautar kasa (NYSC) ba gaskiya bane.

Dubawa ta rahoto cewa binciken kwakkwafi da aka yi kan rantsar da Tinubu ya nuna cewa bai taba yin wannan sanarwar a jawabinsa ba.

Asali: Legit.ng

Authors:
Aisha Musa avatar

Aisha Musa (Hausa writer) Aisha Musa 'yar jarida ce wacce ta kwashe shekaru biyar tana aikin gogewa a harkar yada labarai. Ta kammala karatun ta a Jami'ar Ibrahim Badamasi Babangida (IBB Lapai) a shekarar 2014 tare da digirin farko a fannin Tarihi. Aisha Editan Hausa ce wacce ke amfani da kwarewa da kwazonta don karfafawa wasu gwiwar yin aiki tukuru don cimma nasara. Ta karbi lambar yabo na gwarzuwar shekarar 2021 a bangaren Hausa na Legit. Za ku iya aika mata sakonnin imel ta adireshinta aisha.musa@corp.legit.ng