Farfesa Isa Pantami Ya Fara Shirye-Shiryen Sauka Daga Kujerar Ministan Sadarwa, Bayanai Sun Fito

Farfesa Isa Pantami Ya Fara Shirye-Shiryen Sauka Daga Kujerar Ministan Sadarwa, Bayanai Sun Fito

  • Ministan ma'aikatar sadarwa da tattalin arziƙin zamani ta ƙasa, Sheikh Farfesa Isa Ali Pantami ya fara shirye-shiryen kwashe kayansa daga ma'aikatar
  • Pantami ya bi sahun wasu daga cikin ministocin da suka fara kwashe kayayyakinsu daga ofis gabanin ranar 29 ga watan Mayu da za a rantsar da sabuwar gwamnati
  • Ministocin dai na hannanta ayyukan ma'aikatun da suke jagoranta ne ga manyan sakatarorin dindindin na ma'aikatun

Abuja - A cikin kwanakin da suka rage na shugaban ƙasa Muhammadu Buhari ya kammala wa'adinsa, ministoci sun fara miƙawa manyan sakatarorin dindindin na ma’aikatunsu kujerunsu gabanin rushe majalisar ministocin.

A ranar Litinin, 29 ga watan Mayu 2023, wa'adin mulkin shugaba Buhari na shekaru takwas, wanda ya fara daga ranar 29 ga watan Mayun 2015 zuwa yau zai zo ƙarshe.

Kara karanta wannan

Sarkin Musulmi Ya Ba Bola Tinubu Muhimmiyar Shawara Mai Ratsa Jiki Ana Dab Da Rantsar Da Shi

Pantami ya fara shirye-shiryen barin ofis
Sheikh Isa Pantami Ya Fara Shirye-Shiryen Sauka Daga Kujerar Ministan Sadarwa. Hoto: Professor Isa Ali Pantami
Asali: Facebook

Pantami ya aiwatar da aikinsa na ƙarshe a makon da ya gabata

Ministan ma'aikatar sadarwa da tattalin arziƙi, Farfesa Isa Ali Ibrahim Pantami, ya gudanar da aikinsa na kusa da ƙarshe a makon da ya gabata lokacin da ya kaddamar da wani kwamiti kan kuɗaɗen yanar gizo (blockchain) a Abuja.

LURA: Shin kana son bamu labari da tattaunawa da marubutanmu? Tuntubemu a info@corp.legit.ng

Haka nan ma yau Laraba, ministan ya wakilci shugaban ƙasa wajen wani taron ci-gaban tattalin arziƙi da aka gudanar a ma'aikatar kamar yadda ya wallafa a shafinsa na Fesbuk.

Kamar yadda wasu ministocin suka fara shirye-shiryen barin ofis, alamu na nuni da cewa shima ministan sadarwar ya fara haɗa kayansa don barin ofis.

Daily Trust ta ce wani da ke aiki a ma'aikatar sadarwa ta ƙasa, ya bayyana cewa ya ga ma'aikatan ofishin ministan na kwashe takardu da wasu kayayyakinsa daga ofis a ranar Litinin ɗin da ta gabata.

Kara karanta wannan

Da Dumi-Ɗumi: Gwamnatin Buhari Ta Ayyana Hutun Kwana 1 Saboda Bikin Rantsar da Tinubu

Minista ya bada umarnin a rushe kasuwar UTC

Sai dai shi a nasa ɓangaren, ministan babban birnin tarayya, Malam Muhammad Bello, ya bayar da umarnin rusa shaguna a babbar kasuwar UTC da ke Area 10, da kuma wasu gidaje a Gishiri da dai sauransu.

An ce har yanzu dai ministan yana zuwa ofis domin aiwatar da wasu ayyuka a hukumance.

Buhari ya naɗa sabbin muƙamai a ƙasa da kwana bakwai kafin rantsuwa

A wani labarin na daban kuma, shugaba mai barin gado Muhammadu Buhari ya naɗa wasu sabbin muƙamai guda shida, duk da yana a satin ƙarshe na wa'adinsa.

Daga cikin waɗanda aka naɗa a sabbin muƙamai akwai dakta Steven Andzenge da aka bai wa shugabancin NDPHCL.

Asali: Legit.ng

Online view pixel