Likitocin Najeriya Sun Ba Buhari Wa’adin Makwanni 2 Don Fara Aiwatar da Yajejeniyar da Suka Kulla

Likitocin Najeriya Sun Ba Buhari Wa’adin Makwanni 2 Don Fara Aiwatar da Yajejeniyar da Suka Kulla

  • Kungiyar likitoci a Najeriya ta yi barazanar yin yajin aiki idan gwamnati bata biya musu bukatunsu da suka gabatar ba
  • Kungiyar na neman a fara ware 15% na kasafin kudin Najeriya tare da tura shi ga fannin lafiya saboda wasau dalilai
  • Hakazalika, suna neman a kara albashin ma’aikata likitoci da 200% na adadin kudin da ake biyan likitocin kasar a yanzu

Abeokuta, jihar Ogun - Alamu na nuna kasar nan za ta rikice da yajin aikin likitoci idan gwamnatin Buhari bata gaggauta daukar mataki cikin kankanin lokaci ba.

Wannan zai faru ne sakamakon gargadin da kungiyar likitoci masu neman kwarewa ta Najeriya ta yi na cewa, gwamnatin ta gaggauta fara aikwatar da yajejeniyar da suka cimma a baya.

A cewar rahoton da muka samo, kungiyar ta ba da makwanni biyu a matsayin wa’adin da gwamnati ya kamata ta fara aiwatar da bukatunsu.

Kara karanta wannan

Lauje cikin nadi: Shehu Sani ya tona asirin Buhari, ya fadi gaskiyar dalilin dage kidaya

Likitoci za su tafi yaji idan ba a dauki mataki ba
Likitocin Najeriya lokacin da suke zanga-zanga | Hoto: bbc.com
Asali: UGC

A makon da ya gabata, kungiyar ta yi taro a babban asibitin tarayya da ke Abeokuta ta jihar Ogun, inda anan ne ta bayyana wannan garggadin.

DUBA: Shigo shafin Legit.ng na manhajar Legit.ng na Telegram! Kada ka bari komai ya wuce ka

Meye suke bukata?

A cewar rahoton gidan talabijin na Channels, likitocin na neman gwamnati take ware 15% cikin 100% na kasafin kudin shekara ga fannin lafiya.

A baya gwamnatin na ware 15% ne kacal ga fannin lafiya a duk kasafin da ke fita a shekara, kamar yadda rahotanni suka bayyana.

A cewar kungiyar, sanya 15% ga fannin ne zai magance matsaloli da yawa da ma’aikatan lafiya ke fuskanta a halin da ake ciki.

Matsalolin da suka yiwa fannin katutu

Daga cikin matsalolin da kungiyar ta fitar tace sun yiwa ma’aikatar lafiya da fannin katutu akwai rashin daukar ma’aikatan da za su maye gurbin da ake dashi a fannin.

Kara karanta wannan

1 Ga Watan Mayu: Gwamnatin Tarayya Ta Ayyana Litinin a Matsayin Hutu Don Bikin Ranar Ma’aikata

A bangare guda, kungiyar ta bayyana bukatar a yi gyara ga albashin ma’aikatan kiwon lafiya cikin gaggawa, inda suke bukatan karin 200% na albashin likitoci na yanzu, rahoton BBC News.

Ba yau aka fara ba, kungiyar likitocin na kai ruwa rana da gwamnatin tun shekarun baya, inda yanzu bukatar a sake albashin mambobinta da aka rikci a shekarun 2014, 2015 da 2016.

A wani labarin, kunji yadda gwamnati ta ware ranar Litinin mai zuwa domin yin murnar ranan ma’aikata, inda ta ba da hutun kwana daya ga ma’aikatan kasar.

Asali: Legit.ng

Authors:
Salisu Ibrahim avatar

Salisu Ibrahim (Head of Hausa Desk) Salisu holds BSc in IT (IOU, 2021) and is AfricaCheck's ambassador. He brings over five years of experience in writing, publishing and management. Trained by prestigious newspapers like Reuters, AFP, and Solutions Journalism Network, he curates news stories for the Hausa-speaking audience. He rose from Hausa Editor to Head of Desk at Legit. His commitment to excellence has earned him recognition, including the 2021 Best Hausa Editor award and the Legit Fearless Team Player of the Year 2023.