'Yan Sanda Sun Sheke ’Yan Bindiga 2 a Lokacin da Suka Yi Yunkurin Sace Dan Kasuwa a Katsina

'Yan Sanda Sun Sheke ’Yan Bindiga 2 a Lokacin da Suka Yi Yunkurin Sace Dan Kasuwa a Katsina

  • ‘Yan sandan jihar Katsina sun yi nasarar sheke wasu ‘yan bindigan da suka nufi sace wani dan kasuwa a jihar
  • Wannan ya faru ne a lokacin da tsagerun ke kokarin sace wani dan kasuwa a jihar da ke Arewa maso Yamma
  • An bangare guda, wasu tsagerun ‘yan bindiga sun harbe matasa biyu a jihar Zamfara bayan sace su a daji

Jihar Katsina - Rundunar ‘yan sandan jihar Katsina a jiya Juma’a tace jami’anta sun dakile wani mummunan hari tare da kashe wasu ‘yan ta’adda biyu.

Wannan na fitowa ne daga bakin kakakin rundunar ‘yan sandan jihar, CSP Gambo Isah, kamar yadda jaridar Leadership ta ruwaito.

A cewarsa, jami’an sun dakile harin ne bayan samun bayanan sirri na yadda ‘yan ta’addan ke kokarin sace mutane.

Yadda 'yan sanda suka sheke 'yan bindiga a Katsina
Jihar Katsina da ke Arewa maso Yammacin Najeriya: | Hoto: channelstv.com
Asali: UGC

Ya kara da cewa, bayanan na sirri sun kai ga jami’an Anti-Kidnapping Unit suka lallasa gungun ‘yan bindigan da suka dade a jadawalin nema na jami’an tsaro.

Kara karanta wannan

Innalillahi: 'Yan bindiga sun kashe yaran da suka sace a Arewa, sun sako wasu 70

DUBA: Shigo shafin Legit.ng na manhajar Legit.ng na Telegram! Kada ka bari komai ya wuce ka

‘Yan bindiga na kokarin sace dan kasuwa, sun bakunci kiyama

Ya kuma bayyana cewa, an dakile harin ne a lokacin da tsagerun ke kokarin sace wani fitaccen dan kasuwa a jihar.

A cewar sanarwar, an gano gawar wani kasurgumin dan bindigan da ake zargin yana da hannu a wani harin da aka kai a 2020 a karamar hukumar Malumfashi ta jihar Katsina, rahoton This Day.

A cewar wani yankin sanawar:

“An kashe ‘yan bindiga biyu an kuma kwace bindigogi kirar AK-47.
“A wurin da lamarin ya faru, an ga gawar wani Samaila Shehu da kauyen Tsaunin Kura, a karamar hukumar Malumfashi, fitaccen dan bindigan da aka kama a 2020 da hannu a harin makarantar ma’aikata ta GSS Malumfashi, Katsina kuma aka gurfanar dashi a kotu.”

An kashe yara 2, an sako 70 cikin 85 da aka sace a Zamfara

Kara karanta wannan

1 Ga Watan Mayu: Gwamnatin Tarayya Ta Ayyana Litinin a Matsayin Hutu Don Bikin Ranar Ma’aikata

A wani labarin, kunji yadda aka sace wasu yara a jihar Zamfara, inda daga baya aka sako su bayan karbar kudin fansa.

An kuma ruwaito cewa, an kashe biyu daga cikin yaran da aka sacen, wanda daga baya aka sako 70 cikin 85, inji rahoton majiya daga jihar.

Ya zuwa yanzu, ‘yan sandan jihar Zamfara basu ce komai game da wannan lamarin ba, amma majiya ta tabbatar.

Asali: Legit.ng

Authors:
Salisu Ibrahim avatar

Salisu Ibrahim (Head of Hausa Desk) Salisu holds BSc in IT (IOU, 2021) and is AfricaCheck's ambassador. He brings over five years of experience in writing, publishing and management. Trained by prestigious newspapers like Reuters, AFP, and Solutions Journalism Network, he curates news stories for the Hausa-speaking audience. He rose from Hausa Editor to Head of Desk at Legit. His commitment to excellence has earned him recognition, including the 2021 Best Hausa Editor award and the Legit Fearless Team Player of the Year 2023.