'Yan Bindiga Sun Kai Farmaki Dakin Kwanan Dalibai Mata a Zamfara, Sun Yi Awon Gaba da 2

'Yan Bindiga Sun Kai Farmaki Dakin Kwanan Dalibai Mata a Zamfara, Sun Yi Awon Gaba da 2

  • Rundunar ‘yan sandan jihar Zamfara ta tabbatar da sace wasu ‘yan mata daliban jami’ar tarayya da ke Gusau
  • An ruwaito cewa, ‘yan ta’addan sun kutsa har cikin dakin kwanan dalibai, inda suka yi awon gaba dasu
  • Ya zuwa yanzu, jami’ai na ci gaba da aiki don tabbatar da sun ceto ‘yan matan da kuma kame ‘yan ta’addan

Bungudu, jihar Zamfara - Wasu tsagerun ‘yan bundiga sun sace dalibai mata biyu na jami’ar tarayya da ke Gusau (FUGUS) a jihar Zamfara.

An ruwaito cewa, lamarin ya faru ne da safiyar ranar Lahadi 2 Afirilu, 2023 lokacin da ‘yan ta’addan suka farmaki dakin kwanan daliban da ke Sabon-Gida.

Sabon-Gida dai wani kauye ne da ke kusa da babban kofar jami’ar, kuma ‘yan ta’addan sun daure masu gadin gidan daliban ne kafin aikata barnar satar.

Kara karanta wannan

Innalillahi: Ana tsaka da azumi, 'yan bindiga sun farmaki jihar Arewa, sun kashe jama'a

'Yan bindiga sun sace daliban jami'a guda biyu a Zamfara
Zainab da Maryam, 'yan matan da aka sace a Zamfara | Hoto: dailytrust.com
Asali: UGC

Rahotanni sun ce, ‘yan matan da aka sacen sun hada da wata mai suna Maryam da kuma Zainab, rahoton Channels Tv.

LURA: Shin kana son bamu labari da tattaunawa da marubutanmu? Tuntubemu a info@corp.legit.ng

‘Yan sanda sun tabbatar da faruwar lamarin

Kakakin rundunar ‘yan sandan jihar, Mohammed Shehu ya tabbatar da faruwar lamarin, inda ya bayyana yadda ya faru.

A cewarsa, ‘yan ta’addan sun mamaye dakin kwanan daliban ne da ke kauyen Sabon-gida a karamar hukumar Bungudu da ke jihar ta Arewa maso Yamma, Daily Trust ta ruwaito.

A lokacin da suke barnar, an ce sun daure masu gadin gidan daliban, inda suka kwace wayoyinsu kafin tafiya da daliban da ke karatu a tsangayar kananan kwayoyin halittu (Microbiology).

Bayani daga ‘yan sanda da kuma kokarin da suke yi

A cewar kakakin:

“A lokacin da muka samu rahoto, rundunar ‘yan sanda ta gaggauta zuwa wurin, amma aka tara har ‘yan ta’addan sun tsere da wadanda suka sacen zuwa wani wuri.

Kara karanta wannan

Tashin hankali yayin da 'yan ta'adda suka farmaki 'yan sanda, an sheke tsageru 5

“Kwanishinan ‘yan sanda daga baya ya tura jami’ai domin aikin ceto wadanda aka sacen cikin koshin lafiya, tare da kamo wadanda suka yi barnar da kuma gurfanar dasu a gaban kotu.”

Kakakin ya kara da cewa, kwamishina Kolo Yusuf ya bukaci mazauna da su kwantar da hankali tare da ba ‘yan sanda hadin kai a kokarinsu na ceto ‘yan matan cikin koshin lafiya.

‘Yan ta’adda sun hallaka mutane 5 a Katsina

A wani labarin kuma, kunji yadda ‘yan ta’adda suka hallaka mutane biyar a sabon harin da suka kai wani yankin jihar Zamfara.

Wannan lamari ya zo da tashin hankali, kasancewar wannan ne karon farko da ‘yan bindigan ke yin kisa a yankin.

Majiya ta bayyana yadda lamarin ya faru da kuma yadda ‘yan ta’addan suka yaudari mazauna kamar mutanen kirki.

Asali: Legit.ng

Authors:
Salisu Ibrahim avatar

Salisu Ibrahim (Head of Hausa Desk) Salisu holds BSc in IT (IOU, 2021) and is AfricaCheck's ambassador. He brings over five years of experience in writing, publishing and management. Trained by prestigious newspapers like Reuters, AFP, and Solutions Journalism Network, he curates news stories for the Hausa-speaking audience. He rose from Hausa Editor to Head of Desk at Legit. His commitment to excellence has earned him recognition, including the 2021 Best Hausa Editor award and the Legit Fearless Team Player of the Year 2023.