'Yan Sanda Sun Kwamushe Wasu Masu Satar Yara da Sunan Suna Kai Su Gidan Marayu

'Yan Sanda Sun Kwamushe Wasu Masu Satar Yara da Sunan Suna Kai Su Gidan Marayu

Niger - Rundunar ‘yan sandan jihar Neja ta bankado wasu bata-gari da ke sace yara tare da fakewa da sunan gidan marayu.

Kakakin rundunar ‘yan sandan jihar, Wasiu Abiodun ne ya bayyana bankado gidan tare da kama mutane biyu da ake zargin su ke gudanar da harkallar sace yaran.

Jami'an yan sanda rike da bindigogin
'Yan Sanda Sun Kwamushe Wasu Masu Satar Yara da Sunan Suna Kai Su Gidan Marayu Hoto: Premium Times
Asali: UGC

Wadanda aka kaman sun hada da Saviour Ebuka mai shekaru 20 da kuma Mary Peter ‘yar shekara 25 a yankin Tunga-Maje a karamar hukumar Gwagwalada da ke kusa da babban birnin tarayya Abuja.

Ya bayyana cewa, kama wadannan mutane ya zo ne bayan samun rahoton sun sace wasu yara biyu, kamar yadda aka kai rahoto a ofishin ‘yan sanda na Suleja a jihar Neja.

Karin bayani na nan tafe...

DUBA: Bibiyemu a Instagram don samun labarai masu muhimmanci kai tsaye cikin manhajar

Asali: Legit.ng

Authors:
Salisu Ibrahim avatar

Salisu Ibrahim (Head of Hausa Desk) Salisu holds BSc in IT (IOU, 2021) and is AfricaCheck's ambassador. He brings over five years of experience in writing, publishing and management. Trained by prestigious newspapers like Reuters, AFP, and Solutions Journalism Network, he curates news stories for the Hausa-speaking audience. He rose from Hausa Editor to Head of Desk at Legit. His commitment to excellence has earned him recognition, including the 2021 Best Hausa Editor award and the Legit Fearless Team Player of the Year 2023.