Saraki Ya Garzaya Kasa Mai Tsarki Don Nuna Godiya Ga Allah Yayin da Zai Cika Shekaru 60 a Duniya

Saraki Ya Garzaya Kasa Mai Tsarki Don Nuna Godiya Ga Allah Yayin da Zai Cika Shekaru 60 a Duniya

  • Abubakar Bukola Saraki, tsohon shugaban majalisar dattawa, zai cika shekaru 60 a gobe Litinin
  • Saraki ya tafi kasar Saudiyya domin yin Umara tare da godiya da wannan ni'ima da Allah ya yi masa
  • Masoya sun taya dan siyasar murna da fatan alkhairi, inda wasu da dama suka ce suna kewarsa a majalisa

Saudiyya - A ranar Litinin, 19 ga watan Disamba ne tsohon shugaban majalisar dattawa, Abubakar Bukola Saraki zai cika shekaru 60 a duniya.

Domin raya wannan rana, Saraki ya garzaya kasa mai tsarki don nuna godiya ga Allah madaukakin sarki.

Bukola Saraki
Saraki Ya Garzaya Kasa Mai Tsarki Don Nuna Godiya Ga Allah Yayin da Zai Cika Shekaru 60 a Duniya Hoto: Abubakar Bukola Saraki
Asali: Facebook

Saraki ya rubuta a shafinsa na Facebook:

"Nan da 'yan awanni zan cika shekara 60 a duniya, bisa haka ne na zo birnin Madinah domin yin godiya ga Allah.

LURA: Shin kana son bamu labari da tattaunawa da marubutanmu? Tuntubemu a info@corp.legit.ng

Kara karanta wannan

Mulki har sau 2: Jonathan ya aike da wani muhimmin sako mai daukar hankali ga Buhari

"Ko ba komi, yayin da Allah ya tambaye mu a littafinsa mai tsarki, cikin Surah Ar-Rahman da cewa; "Wanne daga ni'imomin Mahaliccinku ku ke ƙaryatawa? Amsarmu ita ce, BABU!"

Jama'a sun yi martani

Yusuf Bayero ya yi martani:

"Allah ya karba shugaban majalisar dattawa da ya fi kowanne a tarihi Najeriya ina yi maka fatan samun tsawon rayuwa, wadata da kariyar Ubangiji."

Nazir Kabir Hali ya ce:

"Allahu Akba Lallai Sir Kayi Tunani KumaAllah Ysm Sauran Rayuwarka Albarka Ys Ka Cira Duniya Da Lahira Don Annabi Da Al-Qur'ani."

Abdurrahman Mukhtar Tody ya ce:

Masha Allah. Allah qaro masu Albarka, Gaskiya muma Allah ubangiji ya Mana Arziqi."

Suleman Umar Hussain ya ce:

"Allah ya kara shekaru masu albarka, mun yi kewar shugabancinka a majalisar dattawa, yanzu muka san muhimmancin rashinka, Allah ya karo albarka yallabai."

Garba Mustapha ya ce:

"Masha ALLAH Najeriya na kewarka a matsayin shugaban majalisar dattawa saraki."

Muntari Rabi'u Bichi ya yi martani:

Kara karanta wannan

Hukumar EFCC Ta Kai Yaron Gwamnan APC Kotu Bisa Zargin Satar Naira Biliyan 10

"Masha Allah. Alhamdulillah. Allah ya Karo Ma Su Albarka."

Buhari @80: Hadimin Tinubu ya taya shugaban Najeriya murnar zagayowar haihuwarsa

A wani labarin, a ranar Asabar, 17 ga watan Disamba ne shugaban kasar Najeriya, Muhammadu Buhari ya cika shekaru 80 a duniya.

Domin raya wannan rana, hadimin Asiwaju Bola Ahmed Tinubu, dan takarar shugaban kasa na aPC, Joe Ibokwe ya yi shagube ga abokan adawar Buhari.

Ya ce duk da rade-radin ake ta yi cewa ya mutu, yau ga shi Allah ya raya shi har ya kai shekaru 80 a duniya.

Asali: Legit.ng

Online view pixel