"Don Allah Ku Yafe Wa Ɗanmu", Iyayen Aminu Azare Sun Roki Aisha Buhari Ta Yi Masa Afuwa

"Don Allah Ku Yafe Wa Ɗanmu", Iyayen Aminu Azare Sun Roki Aisha Buhari Ta Yi Masa Afuwa

  • Iyaye da yan uwan Aminu Azare, dalibin jami'ar FUD da jami'an tsaro suka kama kan zargin 'zagin' Aisha Buhari sun roki matar shugaban kasar ta yafe wa dansu ta sake shi
  • Shehu Baba-Azare, kawun Aminu ya ce ba su san an kama shi ba bayan kwana biyar da faruwar abin lokacin da abokin karatunsa ya musu waya cew a bai san inda ya ke ba
  • Baba-Azare ya ce mahaifin Aminu ya fada masa cewa ya kira shi ya fada masa an kama shi an kai shi Abuja, an masa duka a gaban matar shugaban kasa an kuma kai shi wani wuri an rufe shi

Iyayen dalibin jami'ar tarayya da ke Dutse, Aminu Azare, wanda aka kama kan zargin matar Shugaba Muhammadu Buhari, Aisha Buhari, 'ta ci kudin talakawa ta koshi' sunyi kira ga first lady din ta yafe wa dansu ta sake shi, rahoton Premium Times.

Kara karanta wannan

Daga Twitter: Matashi ya jefa kansa a matsala, ya shiga hannu bayan zagin Aisha Buhari

An kama Mista Azare, dalibin ajin karshe da ke karanta kula da muhalli da ilimin kimiyyar nazari kan guba (Environmental Management and Toxicology) a jami'ar ne bayan rubutun da ya yi a shafinsa na Twitter a watan Yuni kan zargin Aisha Buhari, ya bazu bayan yan watanni.

Aminu Azare
"Don Allah Ku Yafe Wa Danmu", Iyayen dalibin jami'a da aka kama ya sun roki Aisha Buhari. Hoto: @PremiumTimesNg
Asali: Twitter

Ya lika hoton Aisha Buhari a jikin rubutun da ya wallafa a Twitter.

LURA: Shin kana son bamu labari da tattaunawa da marubutanmu? Tuntubemu a info@corp.legit.ng

Da ya ke magana da BBC Hausa a ranar Litinin, Shehu Baba-Azare, kawun dalibin da aka kama, ya ce iyalan suna rokon matar shugaban kasar ta yi wa dan su afuwa.

Ya ce yan uwansa ba su san an kama shi ba sai bayan kwana biyar da faruwar lamarin, abokin karatun dansu ya fada musu, cewa bai gan shi ba na kwanaki.

Ya ce an kama Aminu a ranar 17 ga watan Nuwamba an kai shi Abuja, inda aka tsare shi kuma aka rika azabtar da shi a gaban Aisha Buhari, Sahara Reporters ta rahoto.

Kara karanta wannan

An Kona Gidan Jigon PDP Awa 24 Bayan Gwamna Ya Masa Kyautar Sabuwar Mota A Babban Jihar Arewa

Kawun ya ce:

"Mahaifinsa bai da masaniya kan kama shi ... da safiyar ranar Litinin, Aminu ya kira mahaifinsa ta lambar jami'in tsaro ya sanar da shi jami'an tsaro sun tsare shi a Abuja. Ya ce an kai shi gidan gwamnati, an masa gargadi tare da dukansa a gaban matar shugaban kasa, kafin aka kai shi wani wurin da bai sani ba aka rufe shi.
"Daga baya mahaifin ya sanar da ni cewa mahukunta jami'an (Jami'ar Tarayya da ke Dutse) sun kira shi sun ce ba su san maganar kamen ba."

Muna rokon Aisha Buhari ta duba Allah ta yafe wa dan mu Aminu ta sake shi - Azare

Kawun ya ce yan uwan suna cikin rudani game da lamarin.

Azare ya ce:

"Tabbas, mun damu. Akwai irin wadannan kamen da har yanzu ba a warware ba. Muna rokon ta ta yafe wa dan mu saboda ita ma mahaifiya ce. Ta yafe masa ta manta da sbin. Muna rokon ta."

Kara karanta wannan

Alkawari kaya: Tinubu ya fadi yadda zai yi da 'yan IPOB idan ya gaji Buhari a 2023

Martanin Kakakin Aisha Buhari Kan Kama Aminu Azare

A lokacin da Premium Times ta tuntubi mai magana da yawun Aisha Buhari, Aliyu Abdullahi, ya ce yana cikin taro.

Bai kuma amsa sakon tes da aka tura masa game da batun ba daga baya.

Kungiyar kare hakkin bil adama ta Amnesty International cikin wata sanarwa da ta fitar ta bukaci a saki dalibin.

Ta ce

"Amnesty International ta bukaci hukumomi su sake shi daga tsarewar da aka masa ba bisa ka'ida ba kuma su tabbatar da cewa an gurfanar da duk wadanda ake zargi da azabtar da shi da cin zarafinsa da aka yi a gaban kotu"

Jami'an tsaro sun kama dalibin da ya ce Aisha Buhari ta ci kudin talakawa - Majiya

Jami'an tsaro da ake kyautata zaton yan sanda ne sun kama Aminu Muhammad Azare bisa yin rubutu yana sukar matar shugaban Najeriya, Aisha Buhari, a Twitter.

Ya yi rubutun ne tun a watan Yunin 2022 amma a baya-bayan nan ya bazu.

Asali: Legit.ng

Authors:
Aisha Khalid avatar

Aisha Khalid (Hausa editor) Aisha Khalid marubuciyar jaridar Legit.ng ce mai fatan shahara. Ta samu digirinta na farko a jami'ar Ahmadu Bello da ke Zaria a shekarar 2018. Ta kwashe shekaru tana rubutu a fannonin siyasa, nishadi, tsegumi da sauransu. Za a iya tuntubar ta a adireshin email din ta kamar haka: aisha.khaleed@corp.legit.ng

Online view pixel