Fitaccen Gwamnan Najeriya Ya Janye Harajin Da Ya Kakabawa Masu Talla, Masu Tura Baro Da Masu Faci A Jiharsa

Fitaccen Gwamnan Najeriya Ya Janye Harajin Da Ya Kakabawa Masu Talla, Masu Tura Baro Da Masu Faci A Jiharsa

  • Farfesa Chukwuma Soludo, gwamnan jihar Anambra ya janye umurnin da ya bada na karbar haraji daga masu talla, masu amalanke da sauransu
  • Soludo ya bayyana hakan ne a yayin da ya ke jawabi wurin taron haraji karo na biyu a gidan gwamnati da ke Awka
  • Gwamnan ya bada umurnin cewa a tabbatar sanarwar ya isa ga wadanda abin ya shafa yana mai cewa bai kamata a rika karbar harajin hannun talakawa ba

Anambra - Gwamnan Jihar Anambra, Farfesa Charles Soludo, ya yi mi'ara koma baya ya soke dukkan harajin da ya saka wa masu tura amalanke, kanikawa, masu talla da sauran ma'aikata a jihar.

Gwamnan ya bada umurnin ne yayin jawabin da yi wa mutanen Anambra a taron hanyoyin samun haraji karo na biyu a gidan gwamnati a Awka, rahoton Daily Trust.

Kara karanta wannan

Yadda Dan Kwallon Najeriya Ya Nutse Bayan Ceto Fasinjojin 5 A Hatsarin Jirgin Ruwa Da Ya Ritsa Da Su

Gwamna Soludo
Soludo Ya Janye Harajin Da Ya Kakaba Wa Masu Talla, Masu Tura Baro Da Masu Faci A Jiharsa. Hoto: @daily_trust.
Asali: Twitter

LURA: Shin kana son bamu labari da tattaunawa da marubutanmu? Tuntubemu a info@corp.legit.ng

A cewar Soludo, masu talla, masu tura amalanke da baro, da kanikawa ba su cikin wadanda za su biya harajin a Jihar Anambra.

A dena karbar haraji daga wurin talakawa masu talla da faci da tura baro - Soludo

Gwamnan ya kara jadada cewa a tabbatar wannan sakon ya isa dukkan kasuwanin jihar Anambra.

Soludo ya ce:

"Masu tura amalanke ba za su biya wani kudi a jihar ba. Masu facin tayoyi a titi suma su dena biyan haraji ga kowa. Masu talla ma su dena biya. A dena matsa wa wannan talakawan.
"Wannan sakon ba na kungiyoyin kasuwanni bane. Idan aka samu hujjan ba su biya, za a soke kungiyar. Muna son gina al'umma inda za a karfafa marasa karfi kuma masu arziki za su iya samun karin kudin don samar da ayyuka da gina arziki."

Kara karanta wannan

Sule Lamido: An Kira Ni Fasto A Arewa Saboda Goodluck Jonathan

Gwamnan Anambra Ya Bada Umurnin A Fara Yi Wa Masu Sana'ar Tura Baro Rajista A Jiharsa

Gwamnan Jihar Anambra, Farfesa Chukwuma Soludo, ya bada umurnin a fara yi wa masu tura baro, direbobin adaidaita sahu, direbobin bas da manyan motocci rajista a jihar.

An tattaro cewa ya dauki matakin ne domin inganta tsaro da kara samar da kuma tabbatar da suna biyan harajinsu a jihar, The Punch ta rahoto.

Sanarwar da sakataren dindindin na Ma'aikatar Sufuri ta Jihar Anambra, Mrs Louisa Ezeanya ta fitar, ya nuna cewa za a fara rajistan ne ta hanyar daukan hotuna da zanen yatsu.

Asali: Legit.ng

Authors:
Aminu Ibrahim avatar

Aminu Ibrahim (Hausa HOD) Aminu Ibrahim leads the Hausa Desk at Legit.ng. He holds a Bachelor's degree in Microbiology from Ahmadu Bello University, Zaria, and pursued further with a Master's degree in Environmental Microbiology from Federal University Dutse, Jigawa. With over seven years of experience, Aminu has honed his craft in news reporting and content editing, weaving narratives that captivate and inspire audiences: aminu.ibrahim@corp.legit.ng or +2348030996164