Ku Kama Mazajenku Da Kyau, Maza Tsada Suke A UK: Budurwa Da Ke Turai Ta Shawarci Yan Matan Najeriya

Ku Kama Mazajenku Da Kyau, Maza Tsada Suke A UK: Budurwa Da Ke Turai Ta Shawarci Yan Matan Najeriya

  • Wata matashiyar budurwa ta shawarci yan matan Najeriya da ke zuwa UK a kan su rike mazajensu da kyau saboda samun miji na da wuya
  • Matashiyar ta bayyana cewa yawancin matan da ke Turai aikinsu suke aure domin samun masoyi na da matukar wahala
  • Mutanen da ke zaune a UK sun cike sashin sharhi don gaskata abun da ta fada game da rayuwar Turai

ABIN LURA: Za ku iya ceton rayuwar diya mace dake cikin hadari. Bada gudunmuwarka ga Patreon na Legit

UK - Wata matashiya yar Najeriya da ke zama a kasar waje ta yi bidiyo a TikTok, tana mai shawartan yan matan Najeriya a kan kada su zo Birtaniya da tunanin samun miji.

Ta bayyana cewa a UK, aiki shine mazajensu. Budurwar ta shawarci yan matan da ke Najeriya a kan su rike mazajensu da kyau.

Budurwa
Ku Kama Mazajenku Da Kyau, Maza Na Tsada A UK: Budurwa Da Ke Turai Ga Yan Matan Najeriya Hoto: TikTok/@queen_fissy77
Asali: UGC

Rayuwar aiki kawai ake yi a UK

Kara karanta wannan

Neman Na Goro: Bidiyon Kyakkyawar Baturiya Tana Tallan Gyada A Titin Lagas Ya Yadu

Mutane sun je sashinta na sharhi don tabbatar da abun da ya fadi game da rayuwar aiki kurum da ake yi a UK.

DUBA: Bibiyemu a Instagram don samun labarai masu muhimmanci kai tsaye cikin manhajar

Kalli bidiyon a kasa:

A daidai lokacin rubuta wannan rahoton, bidiyon ya tattara sharhi sama da 200 da kuma daruruwan “likes”.

Legit.ng ta tattaro wasu daga cikin martanin a kasa:

Thank God ya ce:

“Bamu da lokaci faa. Aikin dare aikin rana. Ya mutum zai yi. Hatta fasto bai ga mabiya ba a ranar Lahadi.”

hotcharles247 ya ce:

“Abun shine saboda yanga da tunkawo ya kashe ku...ku da kuke neman alazawa....lolzzz bari na baki shawara....ki huta ki shirya zuwa bukukuwa...”

Geebaba ya ce:

“Maza na UK kawai dai yawancinku baku san me kuke so bane.”

Tommy-n ta ce:

“Hatta a nan Najeriya babu miji faaa,,,wadanda suka rage yan babi zo gida ne,,,Don haka abun a koina ne.”

Kara karanta wannan

Yadda Budurwa Ta Zama Mai Goge-goge Bayan Kammala Digiri Na Biyu, Allah Ya Sauya Rayuwarta A Karshe

Anthony4133 ya ce:

“Kina neman miji ne ki zo garina.”

‘Yar Asalin Jihar Kogi Ta Lashe Gasar Wacce Tafi Kowa Kyawun Fuska A Najeriya A 2022

A wani labari na daban, mun ji cewa budurwa ‘yar shekaru 20, Isa Deborah ta doke sauran takwarorinta wajen lashe gasar wacce tafi kowa kyawun fuska a Najeriya a 2022.

Taron wanda shine karo na tara ya gudana ne a wajen hada sautin kida na Koga da ke yankin Ikeja ta jihar Lagas a ranar 27 ga watan Agusta kuma kamfanin Zanzy Entertainment ne ya dauki nauyinsa.

Deborah dai ta mallaki digiri a bangaren zamantakewa daga babbar jami’ar Abuja kuma ta kasance haifaffiyar karamar hukumar Kabba/Bunu a jihar Kogi.

Asali: Legit.ng

Authors:
Aisha Musa avatar

Aisha Musa (Hausa writer) Aisha Musa 'yar jarida ce wacce ta kwashe shekaru biyar tana aikin gogewa a harkar yada labarai. Ta kammala karatun ta a Jami'ar Ibrahim Badamasi Babangida (IBB Lapai) a shekarar 2014 tare da digirin farko a fannin Tarihi. Aisha Editan Hausa ce wacce ke amfani da kwarewa da kwazonta don karfafawa wasu gwiwar yin aiki tukuru don cimma nasara. Ta karbi lambar yabo na gwarzuwar shekarar 2021 a bangaren Hausa na Legit. Za ku iya aika mata sakonnin imel ta adireshinta aisha.musa@corp.legit.ng