Yar Najeriya Da Ke Aiki A Dubai Ta Yi Bidiyon Dakin Da Take Rayuwa Da Gadaje Irin Na Yan Makaranta

Yar Najeriya Da Ke Aiki A Dubai Ta Yi Bidiyon Dakin Da Take Rayuwa Da Gadaje Irin Na Yan Makaranta

  • Wata matashiyar budurwa ta nunawa mutane cewa ba jin dadi kawai ake yi a Dubai ba kamar yadda mutane da dama ke tunani
  • Budurwar wacce ke aiki a daular Larabawar ta yi bidiyon dakin da take zama da gadaje mai hawa-hawa irin da dalibai
  • Masu amfani da TikTok da dama sun yi martani yayin da wasu da suka shiga irin wannan yanayi suka gaskata zancenta

Dubai - Wata matashiyar budurwa yar Najeriya mai amfani da shafin @orobosa2020 a TikTok wacce ke aiki a Dubai tana yawan wallafa bidiyoyin halin da take ciki a bangaren aiki a Dubai.

A daya daga cikin bidiyoyin da ta wallafa a shafinta, matashiyar ta fada kan gadonta mai hawa-hawa irin na daliban makaranta bayan aiki. Sannan akwai wani namiji zaune a sama yana karanta littafi hankalinsa kwance.

Kara karanta wannan

Bidiyon Yadda Lakcara Ta Taya Dalibarta Rainon Jinjirinta Yayin da Take Rubuta Jarrabawa

Budurwa
Yar Najeriya Da Ke Aiki A Dubai Ta Yi Bidiyon Dakin Da Take Rayuwa Da Gadaje Irin Na Yan Makaranta Hoto: TikTok/@orobosa2020
Asali: UGC

A wani bidiyon kuma, an gano ta tana daukar gidan don nunawa mutane irin wajen da take rayuwa a kasar waje.

Yawancin bidiyoyin da ke shafinta na dauke da martani ga mutanen da ke mamakin abubuwan da suke gani a shafinta.

LURA: Shin kana son bamu labari da tattaunawa da marubutanmu? Tuntubemu a info@corp.legit.ng

Ga daya daga cikin bidiyoyin a kasa:

A daidai lokacin kawo wannan rahoton, mutum fiye da miliyan daya ne suka kalli bidiyon, ya kuma tattara dubban martani.

Mustafa Ali97917 ya ce:

“Ina ganin mutumin da ke sama yana rayuwa ne a wani birni daban.”

Funmilola Dasilva-Didi ta ce:

“Akalla kina da aikin yi.”

user7531594147592 ya ce:

“Dubai akwai dadi kece baki da kudi.”

@Bigbenny_Ent yace:

“Yallabai ku dukkanku da ke wajen baku mutu ba kada ku sacewa mutane gwiwa da gani kudin akwai tsoka.”

German juice saidya ce:

Kara karanta wannan

Namijin Kirki Ba Zai Yi Soyayya Da Budurwa Fiye Da Shekara Ba Tare Da Ya Aure Ta Ba – Hadimin Gwamna

"Dubai tsaranki ne.”

EVERNICE VICENTIUS ta ce:

"Habibi idan baka da kudi kada ka je dubai.”

Ayyiriri: Yariman Jordan Mai Jiran Gado Zai Angwance Da Kyakkyawar Amaryarsa ‘Yar Saudiyya, Hotuna

A wani labarin, Yariman kasar Jordan mai jiran gado, Hussein bin Abdullah II zai angwance da budurwarsa ‘yar kasar Saudiya, Rajwa Khaled Al-Saif.

Jaridar Zawya ta rahoto cewa an yi baikonsu a ranar Laraba, 17 ga watan Agusta, kamar yadda Kotun masarautar Hashemite ta Jordan ta sanar.

An yi bikin baikon ne a gaban mai martaba sarkin Jordan, Abdullah II, Sarauniya Rania da kuma yan uwan amaryar a garin Riyadh ta kasar Saudiya.

Asali: Legit.ng

Authors:
Aisha Musa avatar

Aisha Musa (Hausa writer) Aisha Musa 'yar jarida ce wacce ta kwashe shekaru biyar tana aikin gogewa a harkar yada labarai. Ta kammala karatun ta a Jami'ar Ibrahim Badamasi Babangida (IBB Lapai) a shekarar 2014 tare da digirin farko a fannin Tarihi. Aisha Editan Hausa ce wacce ke amfani da kwarewa da kwazonta don karfafawa wasu gwiwar yin aiki tukuru don cimma nasara. Ta karbi lambar yabo na gwarzuwar shekarar 2021 a bangaren Hausa na Legit. Za ku iya aika mata sakonnin imel ta adireshinta aisha.musa@corp.legit.ng