Rarara Ya Shirya Taron Saukar Al-qurani Don Samun Zaman Lafiya A Kasar, Jarumai Maza Da Mata Sun Hallara

Rarara Ya Shirya Taron Saukar Al-qurani Don Samun Zaman Lafiya A Kasar, Jarumai Maza Da Mata Sun Hallara

  • Mawakin siyasa Dauda Kahutu Rarara ya shirya taron addu'a na musamman don samun ci gaba da zaman lafiya a Najeriya
  • Rarara ya tara malamai inda suka yi saukar Al-Qur'ani mai girma tare da yin yanka na rakuma
  • Manyan jaruman masana'arta fina-finan Hausa na Kannywood, maza da mata sun hallara a wajen

ABIN LURA: Za ku iya ceton rayuwar diya mace dake cikin hadari. Bada gudunmuwarka ga Patreon na Legit

Shahararren mawakin nan na siyasa kuma shugaban mawakan shugaban kasa Muhammadu Buhari, Dauda Kahutu Rarara ya gudanar da wani taron addu’a na musamman.

Rarara wanda ya kuma kasance jagoran tafiyar 13X13 na masana’antar shirya fina-finan Hausa na Kannywood, ya tara malamai inda aka yi saukar Al-Kur’ani domin ci gaban kasar.

Rarara
Rarara Ya Shirya Taron Saukar Al-qurani Don Samun Zaman Lafiya A Kasar, Jarumai Maza Da Mata Sun Hallara Hoto: malamibrahimsharukhan
Asali: Instagram

Kamar yadda jarumi kuma MC Mallam Ibrahim Sharukan ya wallafa a shafinsa na Instagram, ya ce an yanka rakuma biyu bayan addu’an domin tabbatar da zaman lafiyan kasar.

Kara karanta wannan

Bayan Wuya: Matashi Mai Kafa Daya Wanda Ke Aiki A Wajen Gini Ya Samu Tallafin Karatu A Turai

A cikin bidiyon da ya wallafa a shafin nasa mai suna, an gano taron jama’a da Qur’anai a gabansu suna karantawa, sannan kuma manyan jaruman Kannywood maza da mata duk sun hallara a wajen.

LURA: Shin kana son bamu labari da tattaunawa da marubutanmu? Tuntubemu a info@corp.legit.ng

Kalli bidiyoyin a kasa:

Mawaki Rarara ya yiwa shugaban kasa Buhari wankin babban bargo a sabuwar wakarsa

A wani labarin, munkawo a baya cewa Dauda Kahutu Rarara, ya magantu kan gazawar gwamnati mai ci a wata sabuwar waka.

A cikin wakar, Rarara ya jagoranci wata tawaga ta shahararrun mawakan Hausa karkashin 13X13, wata kungiya ta masana’antar Kannywood.

Lamarin ya haifar da zazzafan martani kan ko babban dan kashenin Buharin baya tare da shi kuma.

Asali: Legit.ng

Authors:
Aisha Musa avatar

Aisha Musa (Hausa writer) Aisha Musa 'yar jarida ce wacce ta kwashe shekaru biyar tana aikin gogewa a harkar yada labarai. Ta kammala karatun ta a Jami'ar Ibrahim Badamasi Babangida (IBB Lapai) a shekarar 2014 tare da digirin farko a fannin Tarihi. Aisha Editan Hausa ce wacce ke amfani da kwarewa da kwazonta don karfafawa wasu gwiwar yin aiki tukuru don cimma nasara. Ta karbi lambar yabo na gwarzuwar shekarar 2021 a bangaren Hausa na Legit. Za ku iya aika mata sakonnin imel ta adireshinta aisha.musa@corp.legit.ng