Kada a Sake Bari Masu Satar Kuɗin Talakawa Su 'Ci Banza', Buhari Ya Gargaɗi Ɓangaren Shari'a

Kada a Sake Bari Masu Satar Kuɗin Talakawa Su 'Ci Banza', Buhari Ya Gargaɗi Ɓangaren Shari'a

  • Shugaba Muhammadu Buhari ya ce duk wata shari’ar rashawa da aka samu matsala wurin uzurorin ayyukanta, alamar tambaya ce ga jajircewar ma’aikatan shari’ar wurin yaki da rashawa
  • A cewarsa, wajibi ne a kama duk wanda aka samu da laifin rashawa da duk wasu laifuka na zagon kasa ga tattalin arziki, kuma a yi gaggawar gurfanar da mai laifin da gamsassun hujjoji don ya fuskanci hukunci
  • Ya yi wannan furucin ne jiya a Abuja yayin bude wani taro na kwana uku da aka yi don wayar da kan ma’aikatan shari’a, masu bincike akan rashawa da masu zartar da hukunci

ABIN LURA: Za ku iya ceton rayuwar diya mace dake cikin hadari. Bada gudunmuwarka ga Patreon na Legit

Abuja - Shugaban kasa Muhammadu Buhari ya ce duk wata shari’ar rashawar da aka samu matsala a wurin ayyukanta saboda wasu uzurori, alama ce ta tambaya dangane da jajircewar ma’aikatan shari’ar kasar nan wurin yaki da rashawa.

Kara karanta wannan

Jihar Bauchi: Gwamna ya yi martani kan zagin Annabi da wata mata ta yi

Ya ce kada a dagawa duk wanda aka kama da rashawa, zagon kasa ga tattalin arzikin kasa da kuma duk wani laifi na kudi kafa daga fuskantar fushin hukuma.

A dena bari masu satar dukiyar talakawa suna kaucewa hukunci, Buhari ya gargadi alkalai
A dena bari masu satar dukiyar talakawa suna kaucewa hukunci, Buhari ya gargadi bangaren shari'a. Hoto: Daily Trust.
Asali: Twitter

Jiya ya sanar da hakan a wurin wani bude wani taro na kwana uku da za a yi a Abuja musamman don wayar da kan ma’aikatan shari’a, masu bincike akan rashawa da kuma mahukunta, mai lakabin ‘Aiwatar da Shari’a: Babbar hanyar yaki da Laifukan zangon kasa ga tattalin arziki.’

LURA: Shin kana son bamu labari da tattaunawa da marubutanmu? Tuntubemu a info@corp.legit.ng

Mustapha ya ce shari’a ta jajirce, kada ta zama ‘yar kallo

Buhari wanda ya samu wakilci Sakataren Gwamnatin Tarayya, Boss Mustapha ya ce ma’aikatan shari’a su yi kokarin cikashe duk wasu gurabun sharia da masu laifukan cikin jama’a su ke boyewa a cikinsu.

Ya kara da jan kunne, inda ya ce:

“Kada shari’a ta tsaya a matsayin ‘yar kallo yayin da masu laifi su ke amfani da damar wurin tserewa da dukiyoyinmu, su kara karfi sannan su bai wa wasu kwarin-gwiwar shiga harkar rashawa.”

Kara karanta wannan

Batanci ga Annabi: Gwamnati ta cire takunkumi a Sokoto, ta haramta zanga-zanga

Shugaban Hukumar Yaki da Rashawa da yi wa Tattalin Arzikin Kasa Zagon Kasa, EFCC, Abdulrasheed Bawa, ya ce EFCC ta shiga damuwa akan yadda ake fadi shari’ar rashawa saboda wasu uzurori na ayyukan shari’a, kamar yadda Daily Trust ta nuna.

Bawa ya ce hakan na iya kawo kokwanto a zuciyoyin mutane

A cewarsa:

“A matsayinmu na hukuma, ba ma sa ran mu ne za mu ci duk wata shari’ar da mu ke yi da wani, amma akwai lokutan da EFCC da ‘yan Najeriya da dama su ke tafka asara akan wasu matakai na shari’a inda wanda ake zargin ya sace kudin al’umma ke samun damar komawa gida ya mori kudaden da ya samu akan wasu azurorin shari’a.
“Akwai yiwuwar hakan ya sanya kokwanto a zuciyoyin jama’a musamman yadda su ka amince da gaskiyar shari’ar Najeriya a ciki da wajen kasar.”

Asali: Legit.ng

Online view pixel