Kundumbala: Farfesan da aka garkame ya yi ‘yunkurin’ bada cin hancin N16m ya na tsare
- Independent Corrupt Practices and Other Related Offences Commission ta na karar John Kester Ifeanyichukwu
- Hukumar ta fadawa kotu cewa Farfesa John Kester Ifeanyichukwu ya nemi ba jami’inta cin hancin Dala $50, 000
- Farfesan ya yi alkawarin zai biya ma’aikacin wadannan kudi saboda a kawo cikas wajen bincikensa da ake yi
Abuja - Hukumar nan ta ICPC ta gurfanar da wani mai suna John Kester Ifeanyichukwu a gaban babban kotun tarayya a bisa zargin laifin bada cin hanci.
The Cable ta ce hukumar ICPC ta na tuhumar John Kester Ifeanyichukwu wanda Farfesa ne a kan yunkurin ba wani ma’aikacinta cin hancin Dala $40, 000.
Kamar yadda darajar Dala ta ke a kasuwar canji a yau, wannan kudi ya haura Naira miliyan 16.
![](https://cdn.legit.ng/images/360x203/db99865dcca40e0f.jpeg?v=1)
Kara karanta wannan
Takarar Amaechi ta na ta karfi, Buratai da tsohon IGP su na mara masa baya a zaben 2023
Wani jawabi da ya fito daga bakin mai magana da yawun ICPC, Azuka Ogugwa a Facebook ya bayyana cewa an kai karar wajen Alkali AO Otaluka a Abuja.
Laifin da ake zargin Farfesan ya aikata shi ne yi wa jami’in hukumar alkawarin fam Dala 50, 000 da gida a Abuja domin ya lalata bincike da ake yi a kansa.
Rahoton ya ce Ifeanyichukwu ya nemi ma’aikacin na ICPC ya karbo masa na’urorinsa da ke hannun hukumar, wadanda ake amfani da su wajen bincike.
DUBA: Bibiyemu a Instagram don samun labarai masu muhimmanci kai tsaye cikin manhajar
![ICPC Abuja ICPC Abuja](https://cdn.legit.ng/images/1120/e5008383b9e5cd5c.jpeg?v=1)
Asali: UGC
Na’urorin sun hada da komfutoci biyu; MacBook S/N CIML8BUGDTY3 da MacBook S/N W80204J7ATN da kuma wayar salula kirar IPhone 11 Pro.
Jawabin kakakin ICPC
“Fadar shugaban kasa ta kawo karar John Kester Ifeanyichukwu a bisa zargin laifuffukan da suka shafi rashin gaskiyam, kwace da kuma satar kudi.
ICPC a kara mai lamba: CR/025/2022, ta sanar da kotu yadda wanda ake zagi ya nemi jami’inta ya sato wayarsa ta IPhone da kuma komfutarsa.
![](https://cdn.legit.ng/images/360x203/145120a7e982063e.jpeg?v=1)
Kara karanta wannan
Jam’iyyar NNPP ta fitar da duk wadanda za su yi mata takaran zaben 2023 a jihar Kano
Za ayi haka da nufin maye gurbinsa da na’urorin karya da hadiminsa zai kawo a madadinsu.”
- Azuka Ogugwa
Alkali ya daga shari'a
Kamar yadda PM News ta kawo rahoto a ranar Talata, hukumar ta na zargin vewa wannan danyan aiki ya sabawa sashe na 18 (b) na dokar ICPC ta 2000.
Mai shari’a ya bada belin Farfesa Ifeanyichukwu a kan N10m bayan ya amsa cewa bai da laifi. Za a cigaba da sauraron karar ne a ranar 21 ga watan Yunin 2022.
Fayemi v Oshiomhole
A makon nan labari ya zo cewa Adams Oshiomhole ya ce Gwamnan jihar Ekiti Kayode Fayemi ya taba nemansa ya murde wani zabe a lokacin yana rike da APC.
Kayode Fayemi ya karyata wannan zargi, ya ce bai taba tunkarar Oshiomhole da maganar magudi ba. Fayemi ya zargi Oshiomhole da karfa-karfa wajen jagoranci.
Asali: Legit.ng