Fusatattun fasinjoji sun toshe filin jirgin Abuja saboda jinkirin tashin jirgi

Fusatattun fasinjoji sun toshe filin jirgin Abuja saboda jinkirin tashin jirgi

  • Wasu fusatattun fasinjoji sun tare kofar shiga filin jirgin Nnamdi Azikiwe da ke Abuja saboda jinkirin tashin jirgi
  • Fasinjojin sun kasance a filin jirgin ne tun a daren ranar Lahadi don shiga jiragensu zuwa wurare daban-daban
  • Sai dai har zuwa safiyar yau Litinin suna nan kara zube ba tare da wani kwakkwaran bayani daga ma'aikatan jirgin ba, lamarin da ya tunzura su

Abuja - Fusatattun fasinjoji masu yawan gaske sun tare kofar shiga filin jirgin sama na Nnamdi Azikiwe da ke Abuja sakamakon tsaikon da aka samu a wajen tashinsu.

Fasinjojin wadanda suka fusata a safiyar ranar Litinin, 9 ga watan Mayu, sun bayyana cewa sun kasance a filin jirgin tun a daren ranar Lahadi domin tashi zuwa wurare mabanbanta.

Fusatattun fasinjoji sun toshe filin jirgin Abuja saboda jinkirin tashin jirgi
Fusatattun fasinjoji sun toshe filin jirgin Abuja saboda jinkirin tashin jirgi Hoto: Premium Times
Asali: UGC

Da misalin karfe 8:36 na safe, fasinjojin kamfanin jirgi na Arik wanda ya kamata su tashi da misalin karfe 7:00 na yammacin ranar Lahadi na nan a wajen zaman matafiya ba tare da wani bayani daga ma’aikata ko jami’an jirgin ba.

Kara karanta wannan

Ta'addanci: 'Yan ta'adda sun bindige jami'an 'yan sanda har 3 a jihar Neja

Wani fasinja ya samar da jaridar Premium Times cewa:

“Sun rigada sun jinkirta shi daga karfe 7 zuwa 9 na daren jiya. Daga 9:45 na jiya har zuwa yanzu.”

Jaridar The Cable ta rahoto cewa fasinjoji sun kwana cike da takaici a filin jirgin yayin da kujerun wajen ne suka zame masu gadajen kwanciya.

Kamfanonin jiragen sama sun hakura, sun fasa tafiya yajin aiki

A gefe guda, mun ji a baya cewa kamfanonin jiragen sama na Najeriya sun dakatar da hukuncinsu na gurgunta bangaren sufurin jiragen sama na Najeriya ta hanyar tafiya yajin aiki a ranar Litinin.

Daily Trust ta ruwaito cewa, shugaban AON, Alhaji Abdulmunaf Yunusa Sarina, wanda ya sanar da hakan a ranar Lahadi, ya ce wannan hukuncin ya biyo baya ne bayan tattaunawa da suka yi da gwamnatin tarayya.

Kara karanta wannan

Nisan kwana: Yadda fasinjan da bai iya tuki ba ya ceto jirgin da direbansa ya rikice a sama

Wannan cigaban ya zo ne bayan a kalla kamfanonin jiragen sama shida sun zare kansu daga yunkurin tafiya yajin aikin a fadin kasar nan.

Asali: Legit.ng

Online view pixel