Ba gaskiya bane ace komai na tafiya dai-dai a Najeriya, inji Obasanjo

Ba gaskiya bane ace komai na tafiya dai-dai a Najeriya, inji Obasanjo

  • Tsohon shugaban ƙasa, Olusegun Obasanjo, ya ce babu abin da ke tafiya dai-dai a Najeriya, amma wataran komai me wucewa ne
  • Sai dai Obasanjo ya bukaci kowane ɗan Najeriya ya ƙara imani da Allah domin wataran zai duba kuma ya yi wa ƙasar nan rahama
  • Tsohon shugaban ya ce ba Najeriya kaɗai bane ke fama da ƙalubale, lamarin ya shafi duniya ne baki ɗaya

Ogun - Tsohon shugaban ƙasa, Olusegun Obasanjo, ya bayyana yaƙininsa cewa ko wane irin muni halin Najeriya ya kai, komai zai zama tarihi watarana, kamar yadda Premium Times ta rahoto.

Obasanjo, wanda ya yi wannan furucin ne a wurin wani taro da Cocin Deeper Life ta shirya a Abeokuta kuma aka watsa shi kai tsaye ranar Talata, ya roki yan Najeriya su ƙara imani da Allah.

Kara karanta wannan

Buhari ya yi Allah wadai da kashe ɗalibar da ta zagi Annabi a Sokoto, ya nemi a yi bincike

Tsohon shugaban ƙasa, Obasanjo.
Ba gaskiya bane ace komai na tafiya dai-dai a Najeriya, inji Obasanjo Hoto: thecable.ng
Asali: UGC

Tsohon shugaban ya ce duba da hali da yanayin da ake ciki, Najeriya da kuma duniya baki ɗaya na buƙatar Allah ya kawo ɗauki, bisa haka ya roƙi 'ya'yan Allah su kai masa kukan su.

Obasanjo ya ce:

Shin kana da labarin da ka/ki ke son an wallafa ma ka/ki? Ka tuntubemu a info@corp.legit.ng!

"Idan ka duba abubuwan dake faruwa birane, jihohin mu, ƙasar mu, nahiyar mu ta Afirka da sauran sassan duniya, baki ɗaya duniya tana bukatar jahadin yanayi."
"Wasu mutane sun zarge mu, Kiristoci da imanin su bai kai ko ina ba, haka duniyar take tun lokacin Annabi Isah, amma hakan na nufin mu cire tsammani? A'a."
"Babu wani lokaci ko wani zamani da aka yi a tarihin duniya wanda ba masu imani bane suka tsaya kai da fata har komai ya wuce."

Ta ya Najeriya zata tsallake wannan yanayin?

Obasanjo ya ƙara da cewa Annabi Nuhu ya tsaya tsayin daka kan aikinsa da imaninsa a lokacinsa, Allah ya kira shi da mutum mai tsoron Allah kuma mai kauce wa saɓo, mutum mai gaskiya.

Kara karanta wannan

Cikakken Labari: Wani Bam Ya Tashi a Masallaci Yayin da Mutane ke tsaka da Sallar Jumu'a

"Ina da yaƙinin cewa saboda irin waɗan nan mutanen kirkin maza da mata Allah zai kalli halin da muke ciki a Najeriya, ya mana rahama."
"Mutane marasa son gaskiya ne kaɗai zasu ce komai na tafiya dai-dai, amma waɗan da suka gaskata Allah suka yi Imani da Annabi Isa, komai zai wuce."
"Mu masu imani duk halin da muka tsinci kan mu duk muninsa kada mu zubar da imanin mu, kuma komai me wucewa ne."

A wani labarin kuma Ana shirin tunkarar 2023 jam'iyyar PDP ta gamu da cikas, Wani Sanata mai ci ya fice daga jam'iyyar

Yayin da kowace jam'iyyar siyasa ke ƙoƙarin dinke ɓarakarta domin tunkarar 2023, PDP ta yi sake Sanata ɗaya tilo daga Oyo ya yi murabus.

Sanata Kola Balogun, mai wakiltar Oyo ta Kudu ya aike wa PDP wasikar murabus daga kasancewarsa ɗan jam'iyya.

Asali: Legit.ng

Authors:
Ahmad Yusuf avatar

Ahmad Yusuf (Hausa editor) Ahmad Yusuf ma'aikacin jaridar Legit.ng sashin Hausa ya fara aiki a 2021, ya kware wajen kawo labarai da rahotanni da suka shafi siyasa da al'amuran yau da kullum. Matashin ɗan jaridar ya koyi Lissafi a digirinsa na farko a Jami'ar Kimiyya da Fasaha da ke Wudil, Kano (KUST) ya kuma samu shaidar kwarewa a fannin aikin jaridar zamani daga Reuters a 2022. Kafin fara aiki da Legit Ahmad ya yi aiki da jaridu da dama na turanci da Hausa tun 2012. Mail: ahmad.yusuf@corp.legit.ng 07032379262