Cikakken jerin yankunan da uwar jam'iyyar APC ta baiwa kujeru a zaben shugabanninta

Cikakken jerin yankunan da uwar jam'iyyar APC ta baiwa kujeru a zaben shugabanninta

Gabanin taron gangamin jam'iyyar All Progressives Congress (APC), an baiwa yankin Arewa maso tsakiyar Najeriya kujeran Shugaban jam'iyya.

Wannan na zuwa ne kwana daya bayan ganawar Gwamnonin jam'iyyar APC da Shugaba Muhammadu Buhari a Abuja don raba kujerun.

Gwamnan jihar Kaduna, Nasir El-Rufa'i, ya ce duk kujerun da yankin Arewa ke rike da su yanzu za'a mayarwa yankin kudu.

Ranar 26 ga Maris aka dage zabe da taron gangamin.

Ga jerin yankuna da kujeran da aka basu:

Kudu maso kudu

(Akwa Ibom, Bayelsa, Cross River, Delta, Edo da Rivers )

Shin kana da labarin da ka/ki ke son an wallafa ma ka/ki? Ka tuntubemu a info@corp.legit.ng!

1. Mataimakin shugaban jam'iyya (na yankin)

2. Kakakin jam'iyya na kasa

3. Shugabar matan jam'iyya

4. Mataimakin ma'ajin jam'iyyar

Kara karanta wannan

Mahadi Gusau da jerin Mataimakan Gwamnonin Jihohi 5 da aka canza daga 2015-2022

5. Mataimakin sakataren nishadi

Kudu maso yamma

(Ekiti, Lagos, Ogun, Ondo, Osun, da Oyo)

1. Sakataren Jam'iyya na kasa

2. Mataimakin shugaban jam'iyya (na yankin)

3. Shugaban matasan jam'iyyar na kasa

4. Mataimakin shugaban Odita na kasa

Kudu maso gabas

(Abia, Anambra, Ebonyi, Enugu, Imo )

1. Mataimakin shugaban jam'iyya (na kudu gaba daya)

2. Mataimakin shugaban jam'iyya (na yankin)

3. Ma'ajin jam'iyya na kasa

4. Shugaban kula da nishadi na kasa

5. Mataimakin sakatren shirye-shirye na kasa

Uwar jam'iyyar APC
Cikakken jerin yankunan da uwar jam'iyyar APC ta baiwa kujeru a zaben shugabanninta
Asali: UGC

Arewa maso gabas

(Adamawa, Bauchi, Borno, Gombe, Taraba da Yobe )

1. Mataimakin shugaban jam'iyya (na yankin)

2. Odita na kasa

3. Mataimakin sakataren kudi na kasa

4. Mataimakiyar shugabar mata na kasa

Arewa maso tsakiya

(Benue, Kogi, Kwara, Nasarawa, Niger, da Plateau )

1. Shugaban jam'iyya

2. Mataimakin shugaban jam'iyya (na yankin)

3. Mataimakin sakatare na kasa

4. Mataimakin mai ada shawara kan harkokin doka

Kara karanta wannan

Da Dumi-Dumi: Kwamishinan gwamnan APC ya fice daga jam'iyya, ya koma PDP

5. Mataimakin Kakakin jam'iyya na kasa

Arewa maso yamma:

(Jigawa, Kaduna, Kano, Katsina, Kebbi, Sokoto da Zamfara )

1. Mataimakin shugaban jam'iyya (na yankin)

2. Lauyan jam'iyya na kasa

3. Shugaban shirye-shirye na kasa

4. Sakataren kudi na kasa

5. Mataimakin shugaban matasa na kasa

Asali: Legit.ng

Authors:
Abdul Rahman Rashid avatar

Abdul Rahman Rashid Rashidah Abdul Rahman 'yar jarida ce kuma dalibar ilimi wacce ta kwashe shekaru kimanin hudu yanzu tare da shararriyar jarida Legit. Ta samu gogewa a ɓangaren rubutun labarai akan fannoni shatta, wanda suka hada da siyasa, kasuwanci, wasanni, nishadi, dss. Zaku tuntubarta a akwatin email: abdulrahman.rashidah@corp.legit.ng