An samu sauyi: Bayan ayyana 'yan bindiga a matsayin 'yan ta'adda, Buhari ya bayyana yadda zai yake su

An samu sauyi: Bayan ayyana 'yan bindiga a matsayin 'yan ta'adda, Buhari ya bayyana yadda zai yake su

  • Tattaunawar shugaban kasa Muhammadu Buhari da gidan talabijin na Channels ya bankado wasu batutuwa masu yawa
  • Daga ciki, shugaba Buhari ya magantu kan matakan da gwamnati ta dauka wajen ganin ta dakile ayyukan 'yan bindiga
  • A bangare guda, gwamnatin ta amince da ayyana 'yan bindiga da masu garkuwa da mutane da sunan 'yan ta'adda a hukumance

Abuja - Shugaban kasa Muhammadu Buhari ya sha alwashin fatattakar ‘yan ta’adda da suka addabi yankin Arewa maso Yamma a kasar, yana mai cewa gwamnati ta riga ta dauki mataki kan hakan.

Buhari ya bayyana hakan ne yayin wata tattaunawa ta musamman da gidan Talabijin na Channels da aka watsa a yammacin jiya Laraba 5 ga watan Janairun 2022.

Shugaban Najeriya ya magantu kan batun 'yan bindiga
Bayan ayyana 'yan bindiga a matsayin 'yan ta'adda, Buhari ya bayyana yadda zai yake su | Hoto: premiumtimesng.com
Asali: UGC

Shugaba Buhari yayin hirar, ya koka kan dalilin da ya sa mutanen da ke da alaka da al'adu iri daya za su yi gaba da juna.

Kara karanta wannan

Daga karshe: Minista ya bayyana hanyar da Buhari zai bi wajen sakin Nnamdu Kanu

A cewar shugaba Buhari:

“Don haka, ina tsammanin yaren da kawai suke fahimta - mun tattauna hakan sosai da hukumomin tabbatar da doka; shugabannin tsaro, Sufeto Janar na 'yan sanda - shi ne a fatattake su; 'yan ta'addan.
"Mun ayyana su 'yan ta'adda, za mu yi maganinsu a haka."

A cewarsa, an samu nasarori a yakin da ake da ‘yan bindiga a yankin, yana mai cewa ya sha ganawa da shugabannin hukumomin tsaro a wani mataki na shawo kan lamarin.

Channels Tv ta ruwaito shugaban na Najeriya yana kara cewa:

"Kuma na yi imanin idan ka je wadannan yankuna na Arewa maso Yamma da Arewa ta Tsakiya a cikin makonni hudu da suka gabata an samu ci gaba a harkar tsaro."

Kalaman shugaban kasar kan ‘yan bindiga a yankunan na zuwa ne a daidai lokacin da Gwamnatin Tarayya ta ayyana masu aikata laifuka a matsayin ‘yan ta’adda.

Kara karanta wannan

Tuna baya: Buhari ya kasa cika alkawurransa saboda bashi da mukarrabai nagari, Bashir Tofa

Meye matakan da gwamnati ke dauka?

Kafin wannan mataki, a karshen shekarar da ta gabata ne babbar kotun tarayya da ke Abuja ta ayyana ‘yan bindiga a matsayin ‘yan ta’adda biyo bayan wani kudiri da gwamnatin tarayya ta shigar a gabanta ta hannun ma’aikatar shari’a.

Wannan ci gaban ya biyo bayan kiraye-kirayen da aka yi daga bangarori da dama kan gwamnati ta ayyana ‘yan bindiga a matsayin 'yan ta'adda.

Baya ga manyan ‘yan Najeriya, majalisar ta kuma bukaci shugaba Buhari da ya ayyana ‘yan bindiga a matsayin ‘yan ta’adda.

A baya ma dai Majalisar Dokokin Jihohi ta yi kira ga Gwamnatin Tarayya da ta haramta ayyukan barayin da suka yi garkuwa da daruruwan mutane tare da kashe wasu a Arewa maso Yamma da Arewa maso Gabas.

A rahotonmu na baya kunji cewa, Gwamnatin tarayyar Najeriya ta ayyana aikin ‘yan bindiga a matsayin aikin ta’addanci a hukumance, kamar yadda FIJ ta tattaro.

Kara karanta wannan

Aiki ga mai yin ka: El-Rufai ya sanar da mataki 1 tak na magance 'yan bindiga

Abubakar Malami, SAN, Babban Lauyan Gwamnatin Tarayya kuma Ministan Shari’a ne ya bayyana hakan yayin da ya bayyana a shirin ‘Barka da Hantsi’ na gidan Talabijin na Najeriya (NTA) a ranar Talata.

Ya ce ofishinsa na aiki don duba hukuncin da kotu ta yanke wanda ya umarci gwamnati ta ayyana ‘yan bindiga a matsayin ‘yan ta’adda.

Asali: Legit.ng

Online view pixel