Yanzu-yanzu: Ranar Litinin zamu dawo da Sabis jihar Zamfara, Matawalle

Yanzu-yanzu: Ranar Litinin zamu dawo da Sabis jihar Zamfara, Matawalle

Gusau - Gwamnan Zamfara, Bello Mohammed Matawalle, ya sanar da cewa ranar Litinin ko Talata za'a mayar da layukan sadarwa da aka kaste a jihar sakamakon matsalar tsaro.

Daily Trust ta ruwaito cewa Matawalle ya bayyana hakan ne yayin zaben Shugabannin jam'iyyar All Progressive Congress APC.

A taron, Gwamnan yace za'a sawo da sabis kuma mutane zasu koma cin kasuwanninsu na mako.

Zaku tuna cewa a ranar 4 ga Satumba an datse sabis domin shawo kan lamarin garkuwa da mutane da ya addabi jihar.

Yanzu-yanzu: Ranar Litinin zamu dawo da Sabis jihar Zamfara, Matawalle
Yanzu-yanzu: Ranar Litinin zamu dawo da Sabis jihar Zamfara, Matawalle Hoto: Zamfara Governor
Asali: Facebook

Shin kana da labarin da ka/ki ke son an wallafa ma ka/ki? Ka tuntubemu a info@corp.legit.ng!

A cewarsa:

"A bayanan da muka samu, an samu saukin hare-haren da ake kaiwa garuruwa kuma nan da Litinin ko Talata, kowa a jihar zai iya waya da jama'a."

Kara karanta wannan

Masarautar Dansadau ta yi zaman sulhu da kasurgumin dan bindiga, Ali Kachalla

"Muna daukan matakan tabbatar da cewa yan ta'adda sun sha wahala. Idan muan wahala, su ma su wahala."

Asali: Legit.ng

Online view pixel