Rikicin Sarauta da Shari’ar Zabe Ba Su Taka Masa Burki ba, An Nada Abba Gwarzon Gwamnoni

Rikicin Sarauta da Shari’ar Zabe Ba Su Taka Masa Burki ba, An Nada Abba Gwarzon Gwamnoni

  • An ayyana gwamnan jihar Kano, Abba Kabir Yusuf a matsayin wanda ya zama jarumin gwamna na shekarar 2024
  • Abba Kabir ya samu karramawar ne bayan kwamitin tantancewa ya zakulo shi tsakanin gwamnonin Najeriya 36 bisa kokarinsa
  • Gwamnatin Kano ta bayyana yadda ta ji da karramawar tare da tare karin haske kan yadda za ta cigaba da ayyukan cigaba a jihar

Editan Legit Hausa Ibrahim Yusuf yana da gogewar aikin jarida da rubuce-rubucen adabi sama da shekaru hudu, kuma kwararre ne a kawo rahotannin kasuwanci, siyasa da lamuran yau da kullum.

Jihar Kano - Duk da rikicin siyasa da sarauta da gwamnan jihar Kano yake fama da su, jaridar This Nigeria ta zaɓe shi a matsayin gwarzon shekara.

A yau ne jaridar ta bayyana Mai girma Abba Kabir Yusuf matsayin gwarzon gwamna a tsakanin sauran gwamnonin jihohi 36.

Kara karanta wannan

Gwamnan Kano ya ware N4.8bn domin gyara makarantu, mutane 17, 000 za su samu aiki

Abba Kabir Yusuf
Abba Kabir Yusuf ya samu lambar yabo. Hoto: Sanusi Bature D-Tofa
Asali: Facebook

Legit ta gano haka ne a cikin sakon da daraktan yada labaran gwamnatin jihar, Sanusi Bature Dawakin-Tofa ya wallafa a shafinsa na Facebook.

LURA: Shin kana son bamu labari da tattaunawa da marubutanmu? Tuntubemu a info@corp.legit.ng

Dalilin karrama Gwamna Abba Kabir Yusuf

Jaridar This Nigeria ta ce an zaɓi Abba a matsayin gwarzon shekara ne bisa yadda ya nuna halin maza wajen kawo cigaba a jihar Kano duk da rikice-rikice da yake fuskanta.

Jaridar ta ce ta naɗa kwamiti domin tantance gwamnonin jihohi 36 amma bayan an kammala auna su a faifai Abba ne ya zama na daya.

Karrama Abba: Martanin gwamnatin jihar Kano

Gwamnatin jihar Kano ta ce karramawar za ta karawa gwamnan ƙarfin gwiwar kawo ayyukan cigaba a jihar.

Kwamishinan yada labaran jihar, Baba Halilu Dantiye ya ce gwamna Abba Kabir zai cigaba da shugabanci da zai zama abin kwatance ga sauran jihohi.

Kara karanta wannan

Gwamna ya yi magana kan yunƙurin tashin bam, ya fallasa masu ɗaukar nauyi

Sauran mutanen da aka karrama

A yayin taron an karrama wasu 'yan siyasa a Najeriya cikinsu akwai ministan Abuja, Nyesom Ezonwo Wike da gwamnan jihar Akwa Ibom.

Jaridar This Nigeria ta shirya taron karramawar ne a wajen murnar cika shekaru 25 kan mulkin dimokuraɗiyya a Najeriya.

Abba zai inganta ilimi a Kano

A wani rahoton, kun ji cewa gwamnatin jihar Kano karkashin gwamna Abba Kabir Yusuf ta ware makudan kudi domin yin ayyuka na musamman a ɓangare ilimi.

Rahotanni sun nuna cewa ayyukan za su shafi dukkan kananan hukumomin jihar guda 44 domin inganta ilimin karkara da birnin jihar.

Muhammad Malumfashi, babban edita a sashen Hausa na Legit ya duba labarin.

Asali: Legit.ng

Authors:
Ibrahim Yusuf avatar

Ibrahim Yusuf (Hausa Editor) Ibrahim Yusuf yana da gogewar aikin jarida da rubuce-rubucen adabi sama da shekaru hudu, kuma kwararre ne a kawo rahotannin kasuwanci, siyasa da lamuran yau da kullum. ibrahim.yusuf@corp.legit.ng

Online view pixel