Abun Tausayi: Wata mata ta hallaka jaririn yar aiki dan wata 5 saboda abu daya

Abun Tausayi: Wata mata ta hallaka jaririn yar aiki dan wata 5 saboda abu daya

  • Wata mata ta shiga hannun yan sanda bisa zargin kashe jaririn yar aikinta ta hanyar hora shi da yunwa a jihar Legas
  • Mahaifiyar jaririn ta bayyana cewa uwar gidanta ta kwace mata yaro ne saboda ta gaza biyan bashin kudin asibitin lokacin haihuwarta
  • Rahoto ya nuna cewa an samu nasarar amso jaririn amma ya mutu yayin da yake kwance a asibiti

Lagos - Jami'an yan sanda sun yi ram da wata mata, Tina Ogbonnaya, bisa zargin kashe wani jariri dan wata biyar da horon yunwa a jihar Legas.

Premium Times ta rahoto cewa Ogbonnaya ta kwace jaririn daga hannun mahaifiyarsa yar shekara 19, wace take mata aiki a gidanta, kan rashin biyan bashi.

A cewar shugaban wata kungiyar kare hakkin bil adama, (BBI), Harrison Gwamnishu, yar aikin Tina ta bayyana cewa ta gaza biyan bashin uwar gidanta kimanin N200,000, wanda ta biya mata yayin da take asibiti.

Kara karanta wannan

Duniya kenan: Dalibar SSS1 ta zuba guda a abincin uwar rikon da ta rene ta tun tana karama

Dan sanda
Abun Tausayi: Wata mata ta hallaka jaririn yar aiki dan wata 5 saboda abu daya Hoto: guardian.ng
Asali: UGC

Ta ƙara da cewa bayan ta haihu, Ogbonnaya ta fara zaluntarta, wanda ya tilasta mata barin gidan amma uwar gidan ta faɗa mata bata isa ta bar gidan ba har sai ta biya bashin.

Ta shaida wa kungiyar BBI cewa, Ogbonnaya ta kwace jaririnta sannan ta kore ta daga gidan kuma duk wani yunkurin amsar jaririn yaci tura, ya zauna hannunta tsawon lokaci ba tare da shayarwa ba.

Shin ta kai rahoto ga yan sanda tun farko?

A cewar mahaifiyar jaririn, da ta kaiwa yan sanda rahoton lamarin da farko ba su ɗauki mataki ba, amma ta samu an dawo mata da yaronta ta hanyar hukumar jin daɗi da walwala ta jihar Legas.

Matar tace jaririn ya dawo hannunta ne rai hannun Allah, kuma ya mutu ne yayin da ake ba shi kulawa a asibitin uwa da yara, ranar Asabar.

Kara karanta wannan

Babbar magana: Wata mata ta rasa aikinta saboda tsananin yin 'Bleaching'

Wane mataki yan sanda suka ɗauka?

Shugaban ƙungiyar BBI, ya tabbatar da cewa a halin yanzun ana tsare da Ogbonnaya a caji ofis ɗin yan sanda na Ajah.

Kazalika kakakin yan sanda na jihar Legas, Adekunle Ajisebutu, bai ɗaga waya ba domin jin cikakken bayani kan lamarin.

A wani labarin na daban kuma miyagun Yan bindiga sun kashe dan Bijilanti, sun yi awon gaba da DSS a Abuja

Wasu yan bindiga da ake zaton masu garkuwa da mutane ne sun sace jami'in hukumar tsaro ta farin kaya (DSS) yayin wani hari kan mutanen yankin Abaji, dake Abuja ranar Asabar.

Yan bindigan sun shiga yankin ne da adadi mai yawa da mutanen su, kuma kai tsaye suka farmaki ofishin jami'an DSS dake yankin.

Asali: Legit.ng

Authors:
Ahmad Yusuf avatar

Ahmad Yusuf (Hausa editor) Ahmad Yusuf ma'aikacin jaridar Legit.ng sashin Hausa ya fara aiki a 2021, ya kware wajen kawo labarai da rahotanni da suka shafi siyasa da al'amuran yau da kullum. Matashin ɗan jaridar ya koyi Lissafi a digirinsa na farko a Jami'ar Kimiyya da Fasaha da ke Wudil, Kano (KUST) ya kuma samu shaidar kwarewa a fannin aikin jaridar zamani daga Reuters a 2022. Kafin fara aiki da Legit Ahmad ya yi aiki da jaridu da dama na turanci da Hausa tun 2012. Mail: ahmad.yusuf@corp.legit.ng 07032379262