"Mutuwa Mai Yankar Kauna": Matashiyar Jarumar Fina Finai Ta Riga Mu Gidan Gaskiya

"Mutuwa Mai Yankar Kauna": Matashiyar Jarumar Fina Finai Ta Riga Mu Gidan Gaskiya

  • Fitacciyar jaruma a masana'antar shirya fina-finai watau Nollywood, Pat Uguwu ta mutu tana da shekara 35 a duniya
  • Abokin aikinta a masana'antar, Jarumi Emeka Okoye ne ya sanar da rasuwar matashiyar a shafinsa yau Laraba, 5 ga watan Janairu, 2025
  • Tuni dai jarumai mata da maza daga Nollywood suka fara tura sakon ta'aziyya da alhinin mutuwar Pat Ugwu tare da yi mata addu'a

Ahmad Yusuf, kwararren edita ne a Legit Hausa da ya shafe tsawon shekaru yana kawo muku rahotannin siyasa, nishadi da al'amuran yau da kullum

Lagos - Masana'antar shirya fina-finai ta Nollywood da ke kudancin Najeriya ta shiga jimami yayin da aka sanar da mutuwar matashiyar jaruma, Pat Ugwu.

Fitacciyar jarumar Nollywood, Pat Ugwu ta riga mu gidan gaskiya tana da shekara 35 a duniya.

Jaruma Pat Ugwu.
Jarumar masana'antar Nollywood, Pat Ugwu ta rasu tana da shekaru 35 Hoto: Emeka Okoye
Asali: Instagram

Matashiyar jarumar Nollywood ta mutu

Wani abokin aikinta, Emeka Okoye, ne ya sanar da mutuwarta a shafinsa na Instagram a ranar Laraba, 5 ga watan Janairu, 2025.

Kara karanta wannan

A hukumance, jam'iyyar APC ta samu ƙarin sanata 1 a Majalisar Dattawan Najeriya

LURA: Shin kana son bamu labari da tattaunawa da marubutanmu? Tuntubemu a info@corp.legit.ng

Okoye ya kuma wallafa takardar tsare-tsaren jana’izarta da ke bayyana yadda za a birne marigayiyar.

Pat Ugwu ta rasa mahaifinta a shekarar 2021, kuma za a yi jana’izarta a ranar 7 ga Fabrairu, 2025.

Emeka Okoye ya nuna alhininsa bisa wannna rashi da suka yi a Nollywood tare da addu'ar Allah ya sa da samu salama.

"Ki huta lafiya, ‘yar uwa. @patpat_ugwu, kenan ba za mu ƙara yin aiki tare ba? Mutuwa ta mana yankan ƙauna, don Allah Ki huta lafiya, Pat. Allah sa ki huta cikin rahamarsa.”

Jarumin ya kuma yi addu’a ga abokan aikinsa:

"Ya Allah, ka kare duk abokan aikina, musamman wadanda nake tare da su. Wannan yawaitar rasuwa tana da ban tsoro. Ina rokon rayuwa ga kowa a wannan shekara ta 2025, Amin."

Manyan jarumai sun miƙa sakon ta'aziyya

Wasu shahararrun jaruman masana'antar Nollywood sun nuna jimaminsu kan wannan rashi.

Destiny Etiko ta rubuta a shafin ta: “Yesu, a’a!!!”

Kara karanta wannan

"Akwai matsala": Majalisar amintattun PDP ta shiga taron gaggawa a Abuja

Kevin Mike ya ce:

“Na tashi da safe kawai na ji labarin mutuwar daya daga cikin ‘yan uwana a masana’antar mu, Pat Ugwu. Ki huta lafiya, masoyiya.”

Haka nan, Rita Edochie, Nkechi Blessing, da wasu da dama sun yi alhini da mutuwar Pat Ugwu.

Ana sa ran jana’izarta za ta tara ‘yan fim da masoyanta domin karramata tare da yi mata addu’a.

Fitaccen jarumin Nollywood ya mutu

A wani labarin, kun ji cewa jarumin fim da ya daɗe ana gogawa da shi a Nollywood, Pa Charles Olumo Sanyaolu ya mutu yana da shekaru 101.

A ruwaito cewa marigayin ya rasu ne lokacin da ya koma barci bayan ya yi ƙorafin cewa yana jin gajiya a tattare da shi.

Muhammad Malumfashi, babban edita a sashen Hausa na Legit ya duba labarin.

Asali: Legit.ng

Authors:
Ahmad Yusuf avatar

Ahmad Yusuf (Hausa editor) Ahmad Yusuf ma'aikacin jaridar Legit.ng sashin Hausa ya fara aiki a 2021, ya kware wajen kawo labarai da rahotanni da suka shafi siyasa da al'amuran yau da kullum. Matashin ɗan jaridar ya koyi Lissafi a digirinsa na farko a Jami'ar Kimiyya da Fasaha da ke Wudil, Kano (KUST) ya kuma samu shaidar kwarewa a fannin aikin jaridar zamani daga Reuters a 2022. Kafin fara aiki da Legit Ahmad ya yi aiki da jaridu da dama na turanci da Hausa tun 2012. Mail: ahmad.yusuf@corp.legit.ng 07032379262

iiq_pixel