Masana'antar Fina Finai Ta Sake Shiga Jimami Bayan Rasuwar Fitaccen Jaruminta

Masana'antar Fina Finai Ta Sake Shiga Jimami Bayan Rasuwar Fitaccen Jaruminta

  • Yayin da ake ci gaba da rasa fitattun jaruman fina-finai, a yau Juma'a an sake sanar da mutuwar wani jarumin a Legas
  • Fitaccen jarumin fina-finan Yarbawa, Ganiyu Oyeyemi wanda aka fi sani da Ogunjimi ya riga mu gidan gaskiya a yau
  • Jarumin fina-finai, Kunle Afod shi ya tabbatar da mutuwar fitaccen jarumin a yau Juma'a 26 ga watan Afrilu a shafin Instagram

Abdullahi Abubakar, Editan Legit Hausa ne a bangaren siyasa, kasuwanci da al'amuran yau da kullum ne, ya na da gogewar aikin jarida sama da shekaru uku.

Jihar Lagos - Masana'antar shirya fina-finan Nollywood ta sake shiga jimami bayan mutuwar fitaccen jaruminta.

An wayi garin yau Juma'a 26 ga watan Afrilu da mutuwar shahararren jarumin fina-finai, Ganiyu Oyeyemi.

Jimami yayin da fitaccen jarumin fina-finai ya kwanta dama
An sake tafka babban rashi yayin da jarumin fina-finan Nollywood, Ogunjimi ya rasu. Hoto: @kunleafod
Source: Instagram

Yaushe jarumin fina-finan ya rasu?

Kara karanta wannan

Katsina: An shiga makoki bayan 'yan bindiga sun hallaka shugaban APC da wani mutum

Marigayin wanda aka fi sani da Ogunjimi ya rasu ne a yau Juma'a 26 ga watan Afrilu bayan fama da jinya.

LURA: Shin kana son bamu labari da tattaunawa da marubutanmu? Tuntubemu a info@corp.legit.ng

Jarumin Nollywood, Kunle Afod shi ya tabbatar da rasuwar marigayin a shafinsa a Instagram a yau Juma'a 26 ga watan Afrilu.

Afod ya ce tabbas masana'antar shirya fina-finan ta tafka babban rashin fitacce kuma jajaritacce.

"Mun yi iya bakin kokarinmu amma Ubangiji ya fi mu sonka, muna maka fatan samun rahama Baba Ogunjimi."

- Kunle Afod

Shura da fitaccen jarumin fina-finan ya yi

Marigayin ya yi kaurin suna a fina-finan jarumta a bangaren yaren Yarbanci inda da ya fito a manyan fina-finai.

Har ila yau, jarumin kafin rasuwarsa yana yawan fitowa a fina-finan tsafi da kuma maita.

Mace-macen taurarin fina-finai a Najeriya

Wannan na zuwa ne yayin da masana'antar shirya fina-finai ke cikin jimamin rashe-rashen da ta yi a cikin kwanaki.

Masana'antar ta tafka manyan rashe-rashe na jarumanta da dama tun farkon wannan shekara da muka ciki.

Kara karanta wannan

An tafka babban rashi yayin da tsohon Sanata ya kwanta dama yana da shekaru 66

Tsohon sanata ya riga mu gidan gaskiya

A wani labarin, kun ji cewa tsohon sanata a Najeriya, Ayogu Eze ya riga mu gidan gaskiya a birnin Tarayya Abuja.

Marigayin wanda ya wakilci mazabar Enugu ta Arewa daga shekarar 2007 zuwa 2015 ya rasu ne a jiya Alhamis 25 ga watan Afrilu.

Sanatan ya ba da gudunmawa sosai a Majalisar Dattawa inda ya kasance daya daga cikin mambobin kwamitin gyara kundin tsarin mulki.

Asali: Legit.ng

Authors:
Abdullahi Abubakar avatar

Abdullahi Abubakar (Hausa editor) Marubuci kuma kwararren ɗan jaridan da ya shafe shekaru 5 yana rubutu a fannin siyasa da harkokin yau da kullum. Ya kammala digirin farko a jami'ar Maiduguri. Ya samu horon aikin jarida a Reuters da AFP, ya sha halartar tarukan karawa juna sani game da bincike da adabi. Tuntube shi a abdullahi.abubakar@corp.legit.ng.