Yaki Ya Yi Tsanani: Kasashen Larabawa Sun Fara Kauce wa Taimakon Amurka
- Kasashen Larabawa suna fara kauce wa Amurka wajen neman sababbin makamai, bayan hare-haren Iran sun rage musu kayan kariya
- Kasashen sun fara komawa kasashe kamar Koriya ta Kudu, Ukraine da Birtaniya domin samun sabbin tsarin kariya, ciki har da makamai masu arha da jirage marasa matuka
- Karancin samar da makamai a duniya, musamman a Amurka, ya sa wadannan kasashe ke neman hanyoyi daban, yayin da bukatar makamai ke karuwa sosai
Abdullahi Abubakar, Editan Legit Hausa ne ta bangaren siyasa, kasuwanci da al'amuran yau da kullum, ya na da gogewar aikin jarida sama da shekaru biyar.
Riyadh, Saudi Arabia - Bayan makonni shida na hare-haren sama masu tsanani, ana samun raguwar makamai a yankin Gabas ta Tsakiya.
Majiyoyi suka ce makaman kariya daga hare-hare a Gabas ta Tsakiya sun ragu sosai, lamarin da ya sa kasashe suka fara neman karin makamai.

Source: Facebook
Yayin da ake da tsagaita wuta mai rauni tsakanin Amurka da Iran, ƙawayen Amurka a yankin suna duban duniya domin samun sababbi hanyoyin kariya cikin gaggawa, cewar The Wall Street Journal.
Yadda yaki ya barke tsakanin Iran da Isra'ila
Wannan na zuwa ne yayin da yaki ya barke tsakanin Iran da Isra'ila wacce ke samun goyon bayan Amurka karkashin Donald Trump.
An fara kai hari ne a ranar 28 ga watan Fabrairun shekarar 2026 a birnin Tehran wanda ya yi ajalin mutane da dama tare da barnata wurare masu muhimmanci a kasar.
Harin ya yi sanadin mutuwa marigayi tsohon jagoran addini a Iran, Ayatollah Ali Khamenei da wasu manyan jami'an tsaro wanda ya sauya salon yaki baki daya.
Daga bisani, Iran ta yi martani mai zafi inda ta kai hare-haren ramuwar gayya kan Isra'ila da Amurka wanda ya jawo wa ƙasashen asara mai yawa.

Source: Getty Images
Kasashen Larabawa sun fara neman mafita
Saudiyya, Qatar da Hadaddiyar Daular Larabawa suna komawa tsarin kariya na Koriya ta Kudu, jiragen Ukraine da bindigogin Gatling, tare da duba sababbin makamai daga kamfanonin Birtaniya.
Hakan ya nuna yadda hare-haren Iran suka girgiza kasashen Gulf, da kuma yadda jirage marasa matuki masu arha ke bai wa hare-hare damar kai wa da yawa.
Rashin isasshen samar da makamai a duniya, musamman bayan yakin Ukraine, na iya sa masana’antun Amurka su rasa damar samun kwangiloli masu yawa nan gaba.
Kasashen Gulf suna ci gaba da neman sababbi hanyoyi, ciki har da hadin gwiwa da Ukraine da sauran kasashe, domin ƙarfafa tsaronsu cikin gaggawa da dorewa.
Kasashen Gulf suna ci gaba da neman sababbi hanyoyi, ciki har da hadin gwiwa da Ukraine da sauran kasashe, domin ƙarfafa tsaronsu cikin gaggawa da dorewa.
Iran ta koka kan game da tsagaita wuta
Mun ba ku labarin cewa mataimakin shugaban ƙasa na farko na Iran, Mohammad Reza Aref ya yi magana kan yiwuwar gudanar da yarjejeniya.
Aref ya ce sakamakon tattaunawar Islamabad zai dogara gaba ɗaya kan fifikon Amurka a tattaunawar zaman lafiya domin kawo maslaha a yakin da ake yi.
Ya bayyana cewa yarjejeniya mai amfani ga ɓangarorin biyu na yiwuwa idan Amurka ta mai da hankali kan muradunta na fifita kanta.
Asali: Legit.ng

