Amurka Ta Saki Kadarorin Iran da Ta Rike kafin Fara Tattaunawa? Magana Ta Fito

Amurka Ta Saki Kadarorin Iran da Ta Rike kafin Fara Tattaunawa? Magana Ta Fito

  • Wani rahoto da aka fitar ya yi ikirarin cewa Amurka ta amince da sakin kadarorin Jamhuriyar Musulunci ta Iran da ta rike
  • Rahotan ya nuna cewa Amurka ta amince ta saki kadarorin ne wadanda aka rike a kasar Qatar da wasu bankunan kasashen waje
  • Wani babban jami'in Amurka, ya fito ya yi martani kan batun cewa Washington ta amince da sakin kadarorin kafin fara tattaunawa

​Editan Legit Hausa Sharif Lawal yana da kwarewar shekaru wajen kawo rahotannin siyasa, al'amuran yau da kullum, tsegumi da nishadi

Birnin Washington, Amurka - Wani babban jami’in Amurka ya yi magana kan batun cewa Washington ta amincr ta saki kadarorin Iran da aka rike.

Jami'in na Amurka ya ƙaryata rahoton da ke cewa Washington ta amince ta saki kadarorin Iran da aka rike a ƙasar Qatar da sauran bankunan ƙasashen waje.

Iran ta mika bukatar ta wajen Amurka
Shugaba Donald Trump na kasar Amurka Hoto: Donald J Trump
Source: Facebook

Tashar Aljazeera ta kawo rahoton maganar da jami'in ya yi a ranar Asabar, 11 ga watan Afirilun 2026.

Kara karanta wannan

Iran ta dauki wani mataki da ya sa ta shiga gaban Amurka a shirin zaman sulhu a Pakistan

Kasar Iran da Amurka za su tattauna

Tawagar Iran da Amurka sun riga sun isa birnin Islamabad na ƙasar Pakistan domin tattaunawar da ke da nufin kawo ƙarshen yaƙi a Gabas Ta Tsakiya.

Tun da fari, Tehran ta bayyana cewa duk wata yarjejeniyar dindindin ta tsagaita buɗe wuta dole ne ta haɗa da sakin kadarorinta da aka sanya wa takunkumi, da kuma dakatar da yaƙin da Isra’ila ke yi da ƙungiyar Hezbollah a Lebanon.

Iran ta ce Amurka ta amince da bukatarta

Wata majiya daga Iran da ba a bayyana sunanta ba ta shaidawa tashar Reuters cewa Amurka ta amince ta saki kadarorin, kuma wannan matakin yana da alaƙa kai tsaye da tabbatar da tsaro a mashigar Hormuz.

Majiyar, wadda ta buƙaci a sakaya sunanta saboda nauyin maganar, ta ce sakin kadarorin "yana da alaƙa kai tsaye da tabbatar da zirga-zirga cikin aminci ta Mashigar Hormuz," wanda ake sa ran zai zama babban jigo a tattaunawar.

Kara karanta wannan

Duk da fargabar Iran ba za ta halarta ba, ana shirin zaman sulhu da Amurka

Majiyar ba ta faɗi adadin kuɗaɗen da Amurka ta amince za ta saki ba. Sai dai wata majiyar ta daban daga Iran ta ce Amurka ta amince ta saki dala biliyan 6 na kuɗaɗen Iran da ke ajiye a Qatar.

Majiyar ta farko ta yi maraba da wannan mataki (da Amurka ta ƙaryata) a matsayin alamar "gaske" wajen cimma yarjejeniya a tattaunawar Islamabad.

Ta ƙara da cewa wannan na ɗaya daga cikin buƙatun Iran a "saƙonnin da aka aika wa ɓangaren Amurka," kuma Tehran ta samu amincewar Amurka ta sakin kuɗaɗen.

Amurka ta yi magana kan amincewa da bukatar Iran
Shugaban kasar Iran, Masoud Pezeshkian Hoto: @drpezeshkian
Source: Twitter

Wane martani Amurka ta yi?

A cikin wani saƙo daga Fadar White House, wani babban jami’in Amurka ya mayar da martani ga rahoton inda ya ce:

“Ƙarya ne. Ba ma a fara tarurrukan ba tukunna.”

A ranar Asabar ɗin, ofishin Firaministan Pakistan, Shehbaz Sharif, ya bayyana cewa ya gana da Mataimakin shugaban Amurka, JD Vance, a Islamabad, yana mai ƙara da cewa an fara tattaunawar zaman lafiya don kawo ƙarshen yaƙin Gabas Ta Tsakiya.

Jagoran addini na Iran ya samu raunuka

A wani labarin kuma, kun ji cewa sabon jagoran addini na Iran, Mojtaba Khamenei, ya samu raunuka a hare-haren Amurka da Isra'ila.

Kara karanta wannan

Ana murna an tsagaita wuta, Trump ya yi maganar da za ta iya harzuka Iran

Majiyoyi sun bayyana cewa Mojtaba Khamenei ya samu raunuka a fuskarsa da kafafunsa amma yana murmurewa.

Hakazalika, sun bayyana cewa Mojtaba Khamenei yana sane da abubuwan da ke gudana a gwamnatin kasar Iran.

Wanda ya tantance Muhammad Malumfashi, babban edita a Legit.ng.

Asali: Legit.ng

Authors:
Sharif Lawal avatar

Sharif Lawal (Hausa Editor) Sharif Lawal ma'aikacin jarida ne wanda ya samu gogewa a harkar aikin jarida. Ya yi digirinsa na farko a jami'ar Ahmadu Bello (ABU) da ke Zaria. Ya samu horo daga Reuters kan aikin jarida da tantance labarai. Za a iya tuntubarsa ta Sharif.lawal@corp.legit.ng