Kashe Khamenei da Manyan Abubuwa 10 da Suka Faru a Yakin Iran da Amurka a Kwana 40

Kashe Khamenei da Manyan Abubuwa 10 da Suka Faru a Yakin Iran da Amurka a Kwana 40

Wasu muhimman abubuwa da suka ja hankalin duniya sun faru tun bayan fara yakin Iran da Amurka/Isra'ila a ranar 28 ga Fabrairu zuwa ranar 8 ga Afrilun 2026.

Legit.ng Hausa ta bude tasha a manhajar Whatsapp. Kasance tare da mu don samun rahotanni da dumi-dumi!

Editan Legit Hausa Ibrahim Yusuf yana da gogewar aikin jarida da rubuce-rubucen adabi sama da shekaru hudu, kuma kwararre ne a kawo rahotannin kasuwanci, siyasa da lamuran yau da kullum.

Iran - A ranar Asabar, 28 ga watan Fabrairun 2026 kasashen Amurka da Isra'ila suka kaddamar da hare-hare kan Iran, lamarin da ya jawo barkewar yaki a Gabas ta Tsakiya.

Kasar Pakistan ta shiga tsakani wajen ganin a tsayar da yakin na mako biyu a ranar Talata, 8 ga watan Afrilun 2026, bayan kwana 40 ana fafatawa.

Shugaba Donald Trump, Ayatollah Ali Khamenei, da Benjamin Netanyahu
Shugabannin Amurka, Iran da Isra'ila da suka yi yaki a Gabas ta Tsakiya. Hoto: Getty Images
Source: Getty Images

A wannan rahoton, Legit Hausa ta tattaro muku wasu muhimman abubuwa da suka faru a lokacin yakin da ya jawo asarar dukiya da rayuka.

1. Kashe Ayatollah Ali Khamanei

Ranar farko da aka kaddamar da yakin, Isra'ila da Amurka sun hada kai sun kai munanan hare-hare Iran a daidai lokacin da ake tattaunawa.

Kara karanta wannan

Bayan Iran, gwamnatin Trump ta juyo Najeriya, ta yi gargadi kan tsaro

Harin ya yi sanadiyyar mutuwar jagoran addini na Iran, Ayatollah Ali Khamenei da wasu 'yan uwansa ciki har da matar shi da ta rasu daga baya.

Ali Khamenei da matar shi
Ayatollah Ali Khamenei da matar shi da aka kashe a Iran. Hoto: Getty Images
Source: Getty Images

2. Kashe wasu jagororin Iran

Bayan kashe Ayatollah Khamenei, Iran ta cigaba da kai hare-haren ramuwar gayya, inda Amurka da Isra'ila suka cigaba da kai hari su ma.

Hare-haren Amurka/Isra'ila sun kashe wasu daga cikin jagororin Tehran, ciki har da sakataren majalisar tsaron Iran, Ali Larijani.

Ali Larijani da aka kashewa Iran
Babban jami'in Iran, Ali Larijani da aka kashe. Hoto: Getty Images
Source: Twitter

Reuters ta rahoto cewa an kashe kwamandan IRGC, Mohammad Pakpour tare da ministan leken asirin Iran, Esmail Khatib a hare-haren da wasu manyan jami'ai.

3. Kashe sojojin Amurka

Wani abin da ya dauki hankali a yakin shi ne yadda dakarun Iran suka rika kashe wasu daga cikin sojojin Amurka a Saudiyya da wasu kasashe.

Rahoton Military Times ya nuna cewa a cikin kwanaki 40 tun bayan fara yakin, sojojin Amurka 13 sun mutu, yayin da 381 suka jikkata.

Farmakin da harbo jiragen sojojin Amurka a kasashen Gabas ta Tsakiya da makalewar sojan da aka kakkabo jirginsa a Tehran ya dauki hankali sosai.

Kara karanta wannan

Yakin Iran: Amurka ta yi gargadi kan aikin Hajjin 2026

Sojojin Amurka da aka kashe
Yadda aka dauko sojojin Amurka da aka kashe a yakin Iran. Hoto: JD Vance
Source: Facebook

4. Nada Mojtaba Khamenei

Bayan kashe Ayatollah Ali Khamenei, jama'a da dama na jiran ganin wanda zai gaje shi wajen jagorantar kasar Iran a lokacin yakin.

Kwanaki kadan bayan haka, gwamnatin Iran ta sanar da nada dan shi, Mojtaba Khamenei a matsayin sabon jagoran addinin kasar.

Mojtaba Khamenei a Iran
Mojtaba Khamenei kafin zama jagoran addini na Iran. Hoto: Getty Images
Source: Getty Images

5. Maganganun Trump kan cin nasara

Daga cikin abubuwan da suka faru da suka dauki hankali akwai ikirarin shugaban Amurka da ya ke yi cewa ya gama rusa kasar Iran.

Abin da ya sanya lamarin ya ja hankali shi ne yadda Iran ke cigaba da harba makamai da kuma yadda Trump ke neman taimakon kasashen NATO duk da ikirarin cewa ya gama da Tehran.

Shugaba Donald Trump
Shugaba Donald Trump yana wani bayani a Amurka. Hoto: Getty Images
Source: Facebook

6. Rufe mashigar Hormuz

Wani babban al'amari da ya ja hankalin duniya shi ne rufe mashigar Hormuz da Iran ta yi bayan fara yakin, lamarin da ya jawo tashin farashin mai a duniya.

Trump ya nemi kasashe su hadu a bude mashigar amma suka ki, inda da dama suka nemi a yi amfani da diflomasiyya maimakon nuna karfin soja.

Kara karanta wannan

Dara ta ci gida: Harin Isra'ila ya dura kan Yahudawa a Iran

Taswirar mashigar Hormuz
Mashigar Hormuz da Iran ta rufe bayan harin amurka. Hoto: Getty Images
Source: Getty Images

7. Jita-jitar mutuwar Netanyahu

Sakamakon wasu hare-hare da Iran ta kai Tel Aviv, an yada jita-jitar cewa Firaministan Isra'ila, Benjamin Netanyahu ya mutu.

Duk da ya fito ya yi bidiyon cewa yana raye, jita-jitar ta ki karewa, hakan na ya jawo maganganu da zargin cewa da fasahar AI aka yi bidiyon.

Benjamin Netanyahu
Benjamin Netanyahu na wani bayani a Isra'ila. Hoto: Getty Images
Source: Getty Images

8. Ajiye aikin jami'in Trump

BBC ta rahoto cewa babban jami’in yaki da ta’addanci na Donald Trump wato Joe Kent ya yi murabus sakamakon yakin Iran, yana kira shugaban kasar ya sake nazari.

A cikin wata wasika da ya fitar, Joe Kent, ya ce:

“Iran ba ta zama barazana kai tsaye ba ga Amurka.”

Kuma ya yi zargin cewa gwamnatin Trump ta:

“Fara yakin ne sakamakon matsin lamba daga Isra’ila.”
Joe Kent
Donald Trump da hadiminsa da ya yi murabus kan yakin Iran, Joe Kent. Hoto: Getty Images
Source: Twitter

9. Zanga zanga a Iran da Amurka

Yayin da ake cigaba da yakin, miliyoyin mutane sun fito kan tituna a Amurka suna Allah wadai da matakan da Donald Trump ya dauka na fara yakin.

Kara karanta wannan

Babu sulhu da Iran, Amurka da Isra'ila sun yi babbar barna a garuruwa 12 na kasar Musulunci

A gefe guda kuma an hango 'yan Iran da dama suna nuna goyon baya da kasarsu, ciki har da taruwa a wuraren da Donald Trump ya ce zai kai hari.

Zanga zangar adawa da yakin Iran a Amurka.
Wata mata mai adawa da yakin da Donald Trump ke yi da Iran a Amurka a filin zanga-zanga. Hoto: Getty Images
Source: Getty Images

10. Barazanar shafe Iran a duniya

Wani abu da ya dauki hankalin al'ummar duniya a yakin shi ne barazanar Donald Trump na cewa zai shafe Iran a doron kasa idan bata bude Hormuz ba.

Al-Jazeera ra rahoto cewa barazanar Trump ta sanya wasu shugabanni a duniya, ciki har da Fafaroma Leo kira da a kai zuciya nesa da komawa teburin sulhu.

Fafaroma Leo a Vatican
Fafaroma Leo yayin huduba a Vatican. Hoto: Getty Images
Source: Getty Images

Iran da Amurka za su zauna

A wani labarin, mun kawo muku cewa bayan yarda da tsagaita wuta na mako biyu, wakilan Amurka da Iran za su tattauna a Pakistan.

Firaministan Pakistan ya sanar da cewa wakilan kasashen za su zauna a kasar shi a ranar Juma'a, 10 ga watan Afrilun 2026.

Kasashe da dama sun yaba da matakin da Pakistan ta dauka na jawo tsagaita wutar, inda ake fatan hakan zai kawo karshen yakin gaba daya.

Wanda ya tantance Muhammad Malumfashi, babban edita a Legit.ng.

Asali: Legit.ng

Authors:
Ibrahim Yusuf avatar

Ibrahim Yusuf (Hausa Editor) Ibrahim Yusuf yana da gogewar aikin jarida da rubuce-rubucen adabi sama da shekaru hudu, kuma kwararre ne a kawo rahotannin kasuwanci, siyasa da lamuran yau da kullum. ibrahim.yusuf@corp.legit.ng