Ana Wata ga Wata: Amurka Ta Karya Sharudda 3 daga cikin Yarjejeniyar Sulhu da Kasar Iran
- Shugaban Majalisar Iran, Mohammad Bagher Ghalibaf ya lissafa sharudda uku da yake zargin Amurka ta karya a yarjejeniyar tsagaita wuta
- Ya ce wannan ne misalin mai sauki game da dalilin da ya sa kasar Musulunci ta Iran ba ta yarda da alkawurran Amurka
- Duk da wadannan zarge-zarge, Ghalibaf bai bayyana a fili ko Iran ta janye daga yarjejeniyar tsagaita wuta ba ko za ta halarci zaman da aka shirya
Legit.ng Hausa ta bude tasha a manhajar Whatsapp. Kasance tare da mu don samun rahotanni da dumi-dumi!
Ahmad Yusuf, kwararren edita ne a Legit Hausa da ya shafe tsawon shekaru yana kawo muku rahotannin siyasa, nishadi da al'amuran yau da kullum
Iran - Shugaban Majalisar Dokokin Iran, Mohammad Bagher Ghalibaf, ya zargi Amurka da karya wasu muhimman sharudda uku daga ciki 10 da kasar ta gabatar domin tattaunawa.
Wannan zargi dai na zuwa ne kasa da kwana guda bayan cimma yarjejeniyar tsagaita wuta tsakanin bangarorin da ke yaki a Gabas ta Tsakiya.

Source: Getty Images
Tashar NBC News ta ruwaito cewa hare-haren da Isra'ila ta kai a yau Laraba kan kasar Lebanon sun fusata Iran, inda ta yi baranzanar daukar mataki idan Amurka ba ta tsawatar mata ba.

Kara karanta wannan
Tun ba a je ko'ina ba, Shugaba Trump ya canza tsarin tattaunawar Amurka da kasar Iran
Sharuddan da ake zargin Amurka ta karya
Abubuwan da shugaban majalisar Iran ke zargin Amurka ta karya a sharuddan yarjejeniyar tsagaita wutar sun hada da;
1. Ci gaba da kai hare-hare a Lebanon
2. Gano jirgin sama maras matuki (drone) a sararin samaniyar Iran
3. Yunkurin hana Iran ci gaba da shirinta na sarrafa sinadarin uranium
Ghalibaf ya bayyana cewa irin wannan hali na kara tabbatar da rashin amincewar da Iran ke yi wa Amurka tun shekaru da dama da suka shige.
Ya rubuta a shafinsa na X cewa:
“Wannan rashin amincewa da muke da shi kan Amurka ya samo asali ne daga yadda take karya alkawura akai-akai, kuma abin takaici, hakan ya sake faruwa.”
Rikicin Lebanon ya kara dagulewa
A halin da ake ciki, shugabannin Amurka da Isra’ila, Donald Trump da Benjamin Netanyahu, sun jaddada cewa Lebanon ba ta cikin yarjejeniyar tsagaita wuta, abin da ya sa aka ci gaba da kai hare-hare a can.

Kara karanta wannan
Ba boye boye, an ji abin da Saudiyya da wasu kasashe suka yi yayin sulhunta Amurka da Iran
Wannan mataki ya kara dagula lamarin, domin Iran na kallon hakan a matsayin karya yarjejeniyar da aka cimma, in ji rahoton Al-Jazeera.
Takaddama kan shirin uranium na Iran
Fadar White House ta kuma bayyana cewa dole ne Iran ta dakatar da shirinta na sarrafa uranium, wanda ke daya daga cikin manyan abubuwan da ake takaddama a kai.
Ghalibaf ya ce:
“Wannan tushen tattaunawa da aka ce zai yiwu, an riga an karya shi tun kafin a fara.”
Ya kara da cewa a irin wannan yanayi, tsagaita wuta ko shiga tattaunawa tsakanin bangarorin biyu ba abu ne mai ma’ana ba.

Source: Twitter
Duk da wadannan zarge-zarge, Ghalibaf bai bayyana a fili ko Iran ta janye daga yarjejeniyar tsagaita wuta ba, ko za ta ci gaba da shirin tattaunawa da Amurka a kasar Pakistan kamar yadda aka tsara.
Iran ta bai wa Amurka zabi 2
A wani rahoton, kun ji cewa gwamnatin kasar Iran ta bukaci Amurka ta zabi daya tsakanin tsagaita wuta da ci gaba da kai wa juna hare-hare ta hannun Isra'ila.
Ministan Harkokin Waje, Abbas Araghchi ya nuna bacin ran Iran kan hare-haren da Isra'ila ke ci gaba da kai wa kasar Lebanon duk da an tsagaita wuta.
Ya ce a halin yanzu duniya za ta zuba ido ta ga ko Amurka za ta yi biyayya ga sharuddan da aka amince da su na tsagaita wuta ko kuma a'a.
Asali: Legit.ng
