Shugaban Amurka, Trump Ya Cika Mamakin Abin da Ya Gani daga Mutanen Kasar Musulunci Ta Iran
- Shugaban Amurka, Donald Trump ya bayana tsantsar mamaki kan halin da mazauna kasar Iran ke nunawa duk da hare-haren da ake kai masu
- Trump ya ce ya ga mutanen Iran na maraba da hare-haren da Amurka da Isra'ila ke kai wa duk da ana taba kusa da wuraren da suke rayuwa
- Wannan na zuwa me bayan Amurka ta yi nasarar ceto matukin jirginta da ya makale a Iran bayan kakkabo jirgin da yake ciki
Legit.ng Hausa ta bude tasha a manhajar Whatsapp. Kasance tare da mu don samun rahotanni da dumi-dumi!
Ahmad Yusuf, kwararren edita ne a Legit Hausa da ya shafe tsawon shekaru yana kawo muku rahotannin siyasa, nishadi da al'amuran yau da kullum
Amurka - Bayan shafe sama da wata guda ana musayar wuta, shugaban Amurka, Donald Trump ya bayyana abin da ya ba shi mamaki game da mutanen kasar Iran.
Shugaba Trump ya bayyana cewa yadda Iraniyawa ke rokon Amurka ta ci gaba da jefa masu bama-bamai a kusa da gidajen da suke zaune, ya yi matukar ba shi mamaki.

Source: Getty Images
BBC Hausa ta tattaro cewa a wani jawabi da ya gabatar, Trump ya ce abin mamaki ne yadda wasu daga cikin ‘yan Iran ke nuna kamar ba su damu da hare-haren ba.
Halin 'yan Iran ya ba Trump mamaki
Shugaban Amurka ya ce:
“‘Yan Iran da muka gani suna cewa ku ci gaba da jefa mana bam. Duk da cewa bama-bamai na fadawa kusa da gidajensu, suna ci gaba da cewa mu kara, abin mamaki ne matuka."
Trump ya kuma bayyana yadda ya bayar da umarni ga rundunar sojin Amurka da su yi duk abin da ya dace domin ceto wani matukin jirgin saman Amurka da ya shiga hadari a Iran.
A cewarsa, an gudanar da wani aiki na musamman cikin gaggawa wanda ya hada da tura jirage da dama cikin kasar Iran, kuma daga bisani an samu nasarar ceto matukin jirgin.
Ya bayyana wannan aiki a matsayin daya daga cikin manyan ayyukan hadin gwiwar soji da aka gudanar cikin kankanin lokaci kuma aka samu nasara, kamar yadda NBC News ta rahoto.
Barazanar Trump ga kasar Iran
Baya ga haka, Trump ya sake nanata matsayarsa kan Iran, inda ya yi barazanar cewa Amurka na da karfin da za ta iya rusa kasar gaba daya cikin kankanin lokaci idan har rikicin ya kara tsananta.
Ya ce:
“Za mu iya lalata dukkan Iran cikin dare guda, watakila ma a daren gobe.”

Source: Getty Images
Tasirin wannan furuci na Trump
Wannan furuci na Trump na zuwa ne a daidai lokacin da rikicin da ke tsakanin Amurka, Isra’ila da Iran ke kara kamari, lamarin da ke haddasa fargaba a duniya baki daya.
Masana harkokin tsaro da siyasa na ganin irin wadannan kalamai na iya kara dagula al’amura, musamman idan aka yi la’akari da yadda rikicin ya riga ya shafi yankuna da dama a Gabas ta Tsakiya.
An kai wani mataki a sulhun Amurka da Iran
A wani labarin, kun ji cewa Jakadan Iran a Pakistan, Reza Amiri Moghadam ya yi bayani kan halin da ake ciki a kokarin kawo karshen yakin Gabas ta Tsakiya.
Jakadan ya bayyana cewa kokarin da Pakistan ke yi don taimakawa wajen dakatar da yakin Amurka/Isra'ila da Iran ya kai wani mataki mai matukar muhimmanci da kuma sarkakiya.
Duk da bai bayyana lokacin da za a yanke shawara ta karshe ba, amma ya bukaci al'umma da su zama cikin shiri don jin sakamako nan gaba kadan.
Asali: Legit.ng


