Kasashen Afirka 3 da Kasar Isra’ila Ta Taɓa Kai Masu Farmaki a Baya
- Yakin Iran da Isra’ila na ci gaba da tayar da hankali a duniya duba da asarar rayuka da dukiyoyin al'umma da ake yi
- Isra'ila ta taba kai hare-hare a wasu kasashen Afirka a tarihi, lamarin da ya shafi siyasa da tsaron yankin
- A wasu kasashen, an kai hare-haren sama kan masana’antu da ayarin makamai, yayin da a wasu aka gudanar da harin domin ceto fasinjoji
Abdullahi Abubakar, Editan Legit Hausa ne ta bangaren siyasa, kasuwanci da al'amuran yau da kullum, ya na da gogewar aikin jarida sama da shekaru biyar.
Tel Aviv, Israel - Ana ci gaba da yaki tsakanin Iran da Isra'ila da ke samun goyon bayan Amurka karkashin jagorancin Donald Trump.
Rahotanni sun nuna cewa Isra’ila ba ta takaita ayyukan sojinta a Gabas ta Tsakiya kadai ba, domin ta taba kai hare-hare a wasu sassan Afirka.

Source: Getty Images
Kasashen Afirka da Isra'ila ta kai hari
Wadannan hare-hare sun hada da farmaki a Sudan, harin Entebbe a Uganda, da kuma mamayar Masar a lokacin rikicin Suez, cewar Binciken Al Jazeera Centre for Studies.
Majiyoyi sun tabbatar da cewa hare-haren sun yi tasiri mai girma a siyasar yankuna da duniya baki daya.
Legit Hausa ta yi duba kan kasashe da Isra'ila ta taba kai masu hari a yankin Nahiyar Afirka.
1. Sudan: Hare-haren sama da ayyukan sirri
A watan Oktoba na shekarar 2012, NPR ta ruwaito cewa wani jami’in leƙen asirin Isra’ila ya tabbatar da cewa an gudanar da ayyukan soji a Sudan.
Wannan ya biyo bayan zargin da gwamnatin Sudan karkashin Omar Al-Bashir ta yi cewa Isra’ila ta kai hari kan wata masana’antar makamai da ke wajen Khartoum.
Isra’ila ta tura jiragen yaki guda hudu domin kai hari kan wata masana’antar makamai da ke gefen Khartoum da asuba, inda aka kashe mutane biyu tare da jikkata wasu da dama.
Wannan ba shi ne karo na farko ba, a shekarar 2009, an lalata wani ayarin makamai a gabashin Sudan ta hanyar harin sama, cewar rahoton BBC.
A shekarar 2011 kuma, wani harin makami mai linzami kusa da Port Sudan ya kashe mutane biyu, daya daga cikinsu babban mai sayen makamai ne ga Hamas.
Wadannan hare-hare da aka maimaita sun nuna yadda Isra’ila ke kokarin dakile hanyoyin safarar makamai ta Sudan.

Source: Getty Images
2. Uganda: Harin Entebbe
Harin Isra’ila a Entebbe, wanda aka fi sani da 'Operation Entebbe', ya faru a watan Yuli na shekarar 1976.
Bayan an sace jirgin saman Air France da ‘yan ta’adda hudu (Palasdinawa biyu da Jamusawa biyu), an karkatar da jirgin zuwa Entebbe a Uganda, inda Shugaban kasar mai mulkin kama-karya, Idi Amin, ya tarbi ‘yan ta’addan.
‘Yan ta’addan sun bukaci a sako fursunoni da ake tsare da su a Isra’ila da Turai, kamar yadda Daily Monitor ta ruwaito.
A ranar 4 ga Yuli, sojojin Isra’ila na musamman sun kaddamar da wani harin ceto mai hatsari a filin jirgin saman Entebbe.
Sun kubutar da mutane 102 da aka yi garkuwa da su, sun kashe ‘yan ta’adda uku, sannan mutane biyu daga cikin wadanda aka sace sun mutu a yayin musayar wuta.
Wannan aiki ya zama abin koyi a tarihin yaki da ta’addanci, inda ya kara wa Isra’ila karfin gwiwa a kasa, tare da matukar raunana martabar Idi Amin a idon duniya.

Source: Getty Images
3. Masar: Harin rikicin Suez
A ranar 29 ga Oktoba, 1956, Isra’ila ta kai hari kan Masar a lokacin rikicin Suez, rundunonin Isra’ila guda 10 sun kutsa zuwa mashigin ruwan Suez, inda suka fatattaki sojojin Masar.
Biritaniya da Faransa sun shiga rikicin nan da nan, inda suka bukaci a janye sojoji tare da kaddamar da nasu harin soja.
A ranakun 5 da 6 ga Nuwamba, sojojin kasashen biyu sun kwace iko da Port Said da Port Fuad, History.com ta ruwaito labarin.
Sai dai matsin lamba daga manyan duniya, musamman Amurka da kuma Majalisar Dinkin Duniya, ya tilasta tsagaita wuta, daga bisani, sojojin Isra’ila sun janye a watan Maris na shekarar 1957.
Wannan lamari ya zama daya daga cikin manyan hare-haren farko da Isra’ila ta yi a nahiyar Afirka, wanda ke da alaka da fafatawar siyasa da iko kan mashigin ruwan Suez.

Source: Facebook
Yakin Iran/Isra'ila na barazana ga kasashen Afirka
A wani labarin, kun ji cewa hukumar kula da abinci ta duniya ta yi gargadin cewa mutane miliyan 10.4 a Yammaci da Tsakiyar Afirka na iya fuskantar yunwa.
Rikicin Iran da isra’ila tare da Amurka na iya haddasa matsalar abinci a duniya wanda har yanzu ake ci gaba da yi.
Har ila yau, kungiyar inganta noma da abinci ta ce kasashe 31 a Afirka na bukatar tallafin abinci ciki har da Najeriya.
Asali: Legit.ng



