Kasar Iran Ta Kara Azama a Yaki da Isra’ila, Ta Fadi Shirinta kan Jiragen Amurka
- Kasar Iran ta sake sauya salon yakinta da Isra'ila da Amurka a Gabas ta Tsakiya bayan tura sababbin na’urorin kariyar sama
- Hare-haren Amurka da Isra’ila sun kai hari wurare da dama ciki har da tashar nukiliya ta Bushehr da ke kasar
- Rahotanni sun ce dubban mutane sun mutu ko jikkata yayin da rikicin ke kara tsananta a yankin Gabas ta Tsakiya
Abdullahi Abubakar, Editan Legit Hausa ne ta bangaren siyasa, kasuwanci da al'amuran yau da kullum, ya na da gogewar aikin jarida sama da shekaru biyar.
Tehran, Iran - Rahotanni sun bayyana cewa kasar Iran ta tura sababbin tsarin kariya a sama domin kare sararin samaniyarta.
Majiyoyi sun tabbatar da cewa hakan na da nasaba da shirin tinkarar jiragen yakin Amurka yayin da yakin ke kara tsananta.

Source: Facebook
Shirin yakin da Iran ta yi wa Amurka
Hukumomin sojin kasar sun ce tsarin ya taimaka wajen harbo wasu jiragen yaki, tare da alkawarin cewa za su tabbatar da cikakken iko a sararin samaniyarsu, cewar Al Jazeera.
A gefe guda kuma, rahotanni sun nuna cewa hare-haren hadin gwiwar Amurka da Isra’ila sun kai tashar nukiliya ta Bushehr, inda aka tabbatar da mutuwar mutum guda.
Sai dai ba a tabbatar da ko harin ya haifar da zubar lalata injin nukiliyar ba, yayin da ake ci gaba da tattara bayanai kan barnar.
Rahotanni sun kuma ce an harbo wani jirgin yaki na Amurka a sararin Iran, lamarin da ke nuna karuwar arangama kai tsaye tsakanin bangarorin biyu, cewar TRT World.

Source: Twitter
Iran ta harba makamai kasashe makwabta
Wani jami’in Amurka ya tabbatar da harbo jirgin kasar, yayin da ake kokarin ceto matukan jirgin a yankin tsakiyar kasar Iran.
Haka kuma, rahotanni sun ce Iran ta harba makamai masu linzami da jirage marasa matuki da dama kan wasu kasashe makwabta, ciki har da Jordan.
Sai dai dakarun Jordan sun ce sun dakile yawancin hare-haren, duk da cewa wasu sun kai ga wuraren da aka nufa.
Bugu da kari, rahotanni sun nuna cewa hare-haren sun shafi cibiyoyin ilimi da masana’antu a Iran, inda sama da jami’o’i 30 suka gamu da hari tun farkon rikicin.
Adadin mutanen da suka mutu da jikkata ya karu sosai, inda rahotanni ke nuna cewa dubban mutane sun rasa rayukansu yayin da daruruwan dubban suka rasa matsugunansu.
A halin yanzu, kasashe da dama na kira da a dakatar da rikicin tare da komawa kan tattaunawa domin kauce wa karin tabarbarewar lamura.
Iran/Isra'ila: Najeriya da kasashe 39 sun yi zama
A wani labarin, an ji cewa ana tsaka da yaki, kasashe 40 ciki har da Najeriya sun gudanar da taro domin nemo hanyoyin dawo da zirga-zirgar jiragen ruwa a mashigin Hormuz.
Hakan ya biyo bayan matakin rufe mashigar da Iran ta yi dalilin yakin da ake yi tsakanin ta da Isra'ila da Amurka a Gabas ta Tsakiya.
Barazanar hare-haren Iran da ramuwar gayya ta dakatar da zirga-zirga a mashigar, lamarin da ya jawo tashin farashin mai a duniya.
Wanda ya tantance Muhammad Malumfashi, babban edita a Legit.ng.
Asali: Legit.ng

