Kasar Musulunci Ta Iran Ta Sabawa Saudiyya da Najeriya, Ta Sanar da Ranar Karamar Sallah

Kasar Musulunci Ta Iran Ta Sabawa Saudiyya da Najeriya, Ta Sanar da Ranar Karamar Sallah

  • Kasar Musulunci ta Iran ta ayyana ranar Asabar, 21 ga watan Maris, 2026 a matsayin ranar Karamar Sallah bayan kammala azumin watan Ramadan
  • Hukumomin Iran sun sanar da cewa ba a ga jinjirin watan Shawwal ba a yau Alhamis, 29 ga watan Ramadan, dom haka za a cika azumi 30 gobe Juma'a
  • Haka zalika, kasar Iraki ta bi sahun makwafciyarta, ta sanarda ranar Asabar mai zuwa a matsayin ranar idin karamar Sallah

Ahmad Yusuf, kwararren edita ne a Legit Hausa da ya shafe tsawon shekaru yana kawo muku rahotannin siyasa, nishadi da al'amuran yau da kullum

Iran - Hukumomin Jamhuriyar Musulunci ta Iran sun sanar da cewa musulmin kasar za su cika azumi 30 a gobe Juma'a, 20 ga watan Maris, 2026.

Iran ta sanar da cewa ranar Juma’a ce za ta kasance ranar karshe ta watan Ramadan a kasar, yayin da za a fara bikin karamar Sallah (Eid al-Fitr) a washe gari ranar Asabar.

Kara karanta wannan

Bayan sanarwar Saudiyya, Sarkin Musulmi ya fadi ranar da za a yi karamar Sallah a Najeriya

Mojtaba Khamenei.
Jagoran addini na kasar Musulunci ta Iran, Mojtaba Khamenei Hoto: Anadolu
Source: Getty Images

Jaridar Vanguard ta tattaro cewa hakan na kunshe ne a wata sanarwar da ta fito daga ofishin jagoran addinin kasar, Mojtaba Khamenei, da yammacin yau Alhamis.

Sanarwar ta bayyana cewa bayan duban jinjirin wata da aka yi a ranar 29 ga Ramadan, an tabbatar da cewa Juma’a ita ce rana ta 30 ga watan Ramadan mai albarka.

"Gobe Juma'a, za ta kasance rana ta 30 ga watan Ramadan mai albarka, sannan kuma za a yi Eid al-Fitr watau karamar Sallah washe gari, wanda ke nuna ƙarshen lokacin azumi," in ji sanarwar.

Kasar Iraki ta bi sahun Iran

Haka kuma, kasar Iraki wacce mafi yawan al’ummarta ‘yan Shi’a ne, ta bi sahun wannan sanarwa ta Iran, kamar yadda babban malamin Shi’a, Ayatollah Ali al-Sistani ya sanar.

Babban malamin na Iraki ya bayyana cewa sanar da ranar Sallah ta dogara ne da ganin jinjirin watan Shawwal, kamar yadda tsarin kalandar Musulunci ya tanada.

Kara karanta wannan

Azumi ya zo karshe: Daular Larabawa ta sanar da ranar hawan idin karamar Sallah

An nada Mojtaba Khamenei a matsayin sabon jagoran koli na Iran a watan Ramadan, bayan rasuwar mahaifinsa, Ayatollah Ali Khamenei, wanda aka kashe a hare-haren farkon yakin da Amurka da Isra’ila suka kaddamar kan Iran.

A bana, ranar karshe ta Ramadan ta zo daidai da lokacin bikin Nowruz, wanda ake yi a kasar Iran domin nuna farkon bazara, in ji rahoton Arab News.

Sallah.
Musulami na cikin ibadar sallah a masallaci Hoto: Jaafaru Hamad
Source: Getty Images

Muhimmancin Ramadan ga Musulmi

Azumin Ramadan na daya daga cikin rukunan Musulunci guda biyar, inda miliyoyin musulmi a duniya ke azumi daga fitowar alfijir zuwa faduwar rana.

Haka kuma, ana karfafa wa musulmi musamman masu rufin asiri gwiwa domin su taimaka wa talakawa ta hanyar bayar da sadaka domin rage radadin rayuwa ga masu karamin karfi.

Saudiyya ta sanar da ranar Sallah

A wani labarin, kun ji cewa Saudiyya ta tabbatar da cewa ba a samu sahiihin rahoton ganin jinjirin watan Shawwal na shekarar 1447AH ba a ranar Laraba, 29 ga watan Ramadan.

Masarautar Saudiyya ta bayyana cewa musulmi za su cika azumi 30 cif a wannan shekara, tare da ayyana ranar Juma'a, 20 ga watan Maris, 2026 a matsayin ranar karamar Sallah.

Wannan dai na zuwa ne bayan kammala azumin watan Ramadan, wanda bisa ga wannan sanarwa, zai cika kwanaki 30 a bana.

Asali: Legit.ng

Authors:
Ahmad Yusuf avatar

Ahmad Yusuf (Hausa editor) Ahmad Yusuf ma'aikacin jaridar Legit.ng sashin Hausa ya fara aiki a 2021, ya kware wajen kawo labarai da rahotanni da suka shafi siyasa da al'amuran yau da kullum. Matashin ɗan jaridar ya koyi Lissafi a digirinsa na farko a Jami'ar Kimiyya da Fasaha da ke Wudil, Kano (KUST) ya kuma samu shaidar kwarewa a fannin aikin jaridar zamani daga Reuters a 2022. Kafin fara aiki da Legit Ahmad ya yi aiki da jaridu da dama na turanci da Hausa tun 2012. Mail: ahmad.yusuf@corp.legit.ng 07032379262