Ana Rade Radin Ya Mutu, Jagoran Addinin Iran Ya Yi Nadin da Zai Iya Rikita Amurka da Isra'ila
- Jagoran addinin Iran, Mojtaba Khamenei ya nada Mohsen Rezaei, a matsayin mai ba shi shawara kan harkokin sojoji
- Wannan nadi na zuwa ne yayin da Amurka da Isra'ila suka yi ikirarin cewa sun raunata Mojtaba, inda suka ce ba tabbacin yana raye
- Rezaei, mai shekaru 71 da haihuwa ya taba zama shugaban rundunar juyin juya halin Iran watau IRGC, kuma ya rike mukamai daban-daban
Legit.ng Hausa ta bude tasha a manhajar Whatsapp. Kasance tare da mu don samun rahotanni da dumi-dumi!
Ahmad Yusuf, kwararren edita ne a Legit Hausa da ya shafe tsawon shekaru yana kawo muku rahotannin siyasa, nishadi da al'amuran yau da kullum
Iran - Sabon jagoran addini na Jamhuriyar Musulunci ta Iran, Mojtaba Khamenei ya fara nade-naden mutanen da za su taimaka masa wajen gudanar da harkokin mulki.
Mojtaba Khamenei, ya naɗa tsohon shugaban rundunar Juyin Juya Hali (IRGC), Mohsen Rezaei, a matsayin mai ba shi shawara kan harkokin soji.

Source: Getty Images
Tashar Al-Jazeera ta tabbatar da wannan jadi da jagoran Iran ya yi a wani rahoto da ta wallafa shafin X yau Litinin, 16 ga watan Maris, 2026.
Jagoran Iran ya yi muhimmin nadi
Rahotannin kafafen yaɗa labarai na cikin gida a Iran sun tabbatar da cewa an yi wannan naɗi ne bisa umarnin sabon babban kwamandan rundunar sojin ƙasar.
Wannan mataki na zuwa ane yayin da Amurka da Isra'ila suka yi ikirarin illata Mojtaba Khamenei, inda aka ji Shugaba Donald Trump na cewa babu tabbacin yana raye.
Sanarwar ta ce:
“An naɗa Janar Mohsen Rezaei a matsayin mai ba da shawara kan harkokin soji bisa umarnin babban kwamanda kuma jagora na kasa, Ayatollah Mojtaba Khamenei.”
Wanene Mohsen Rezaei?
Rezaei mai shekaru 71 ya taba zama shugaban rundunar IRGC, wacce ake ɗauka a matsayin bangaren akida na rundunar sojin Iran kuma tana da babban tasiri a harkokin tsaro da siyasar ƙasar.
Bayan saukarsa daga shugabancin rundunar, ya rike mukamai daban-daban a cikin gwamnatin Iran, kamar yadda Vanguard ta ruwaito.
Yadda aka samu sauyin jagoranci a Iran
Mojtaba Khamenei mai shekaru 56 ya karɓi mulki ne a farkon wannan watan bayan mutuwar mahaifinsa, tsohon jagoran Ayatollah Ali Khamenei, wanda aka kashe a hare-haren da Amurka da Isra’ila suka kai a ranar 28 ga Fabrairu, 2026.

Kara karanta wannan
An sanar da yanayin da jagoran addinin Iran, Mojtaba Khamenei ke ciki bayan kai masa hari
A zamanin Ali Khamaenei, Yahya Rahim Safavi ne ke rike da mukamin mai ba da shawara kan harkokin soji. Sai dai har yanzu ba a tabbatar ba ko zai ci gaba da rike wannan matsayi a karkashin Mojtaba Khamenei

Source: Twitter
A wata sanarwa da ya fitar ranar Litinin, Mojtaba Khamenei ya umarci dukkan jami’ai da shugabannin hukumomi da mahaifinsa ya naɗa da su ci gaba da gudanar da ayyukansu kamar yadda aka saba.
An kama yan leken asiri 500 a Iran
A wani labarin, kun ji cewa dakarun 'yan sandan kasar Iran sun damke mutane kimanin 500 da ake zargin da yi wa Amurka da Isra'ila leken asiri.
Yan sandan sun ce kusan rabin mutanen da aka kama suna da hannu a manyan laifuffuka, ciki har da ba da bayanan wuraren da ake kai hare- hare a Iran.
Hukumar leƙen asiri ta rundunar sojojin juyin juya hali na Iran ta ce Isra’ila da Amurka na ƙoƙarin tayar da tarzoma da amfani da ‘yan leƙen asiri domin haddasa rikici a cikin kasar.
Wanda ya tantance Muhammad Malumfashi, babban edita a Legit.ng.
Asali: Legit.ng
