Cin Kofin Duniya: Trump Ya Gargadi Kasar Iran kan Shiga Gasar a Amurka
- Shugaban Donald Trump ya yi magana game da yiwuwar shigar tawagar kwallon kafa ta Iran gasar cin kofin duniya
- Trump ya ce ba zai iya ba da tabbacin tsaron tawagar ta Iran ba idan ta zo Amurka domin fafatawa a gasar ta shekarar 2026
- Ministan wasanni na Iran ya ce yakin Amurka da Isra'ila ya sa kasar ba za ta shiga gasar ba saboda hare-haren da aka yi
CHECK OUT: How to Start Earning with Copywriting in Just 7 Days – Even if You’re a Complete Beginner
Abdullahi Abubakar, Editan Legit Hausa ne ta bangaren siyasa, kasuwanci da al'amuran yau da kullum, ya na da gogewar aikin jarida sama da shekaru biyar.
Washington DC, US - Shugaban Amurka, Donald Trump, ya yi magana game da shigar Iran gasar cin kofin duniya da za a yi a Amurka.
Trump ya bayyana cewa ba zai iya ba da tabbacin tsaron tawagar kwallon kafa ta Iran ba idan ta je Amurka domin halartar gasar cin kofin duniya ta shekarar 2026.

Source: Facebook
Amurka: Trump bai da tabbacin tsaron 'yan Iran
Trump ya bayyana hakan ne a wani sako da ya wallafa a shafin sada zumunta na Truth Social wanda a ranar Alhamis 12 ga watan Maris, 2026.
Ya ce tawagar Iran na maraba da shiga gasar kofin duniya, amma yana ganin bai dace su zo ba saboda lafiyarsu da tsaronsu da ake ganin yana cikin hatsari.
Ya rubuta cewa:
“Muna maraba da tawagar kwallon kafa ta Iran na shiga gasar kofin duniya, amma ban ga ya dace su zo ba saboda rayuwarsu da tsaronsu.”
A cewar rahotanni, an shirya Iran ta buga wasanni uku na rukuni a watan Yunin shekarar 2026 a biranen Amurka.
Wasannin sun hada da na karawa da New Zealand da Belgium a Los Angeles, da kuma wasa da Egypt a Seattle.

Source: Twitter
Iran ta fasa shiga gasar cin kofin duniya
Sai dai ministan wasanni na Iran, Ahmad Donyamali, ya ce yakin da Amurka da Israel suka fara da Iran ya sa kasar ba za ta iya shiga gasar ba.
Ya ce kashe babban jagoran Iran, Ayatollah Ali Khamenei, da wasu manyan jami’an gwamnati ya sa ba zai yiwu kasar ta halarci gasar ba.
Donyamali ya bayyana cewa:
“Idan aka yi la’akari da cewa wannan gwamnati ta kashe jagoranmu, babu wani yanayi da zai sa mu halarci gasar kofin duniya da aka shirya yi a Amurka.”
Kasashen Amurka, Canada da Mexico ne za su karbi karbi bakuncin gasar cin kofin duniya ta shekarar 2026 da za a yi tsakanin watan Yuni zuwa Yulin shekarar 2026.
Kofin duniya: Trump ya magantu game da Iran
A wani labarin, kun ji cewa kasar Iran ta yi nasarar shiga gasar cin kofin duniya ta shekarar 2026 wadda za a fafata a kasashen Amurka, Canada da Mexico.
Yakin da ya barke tsakanin Amurka, Iran da Isra'ila, ya kawo kan yiwuwar kasancewar kasar a gasar wadda hukumar FIFA ke shiryawa duk bayan shekaru hudu a duniya.
Shugaba Donald Trump na Amurka ya yi magana kan yiwuwar kasancewar Iran a gasar buga kwallon kafan yayin da ake ci gaba da yaki a Gabas ta Tsakiya.
Wanda ya tantance Muhammad Malumfashi, babban edita a Legit.ng.
Asali: Legit.ng

