Iran Ta Kada Hantar Isra’ila, Ta Fadi Tsawon Lokacin da Za Ta Yi Tana Yakarta

Iran Ta Kada Hantar Isra’ila, Ta Fadi Tsawon Lokacin da Za Ta Yi Tana Yakarta

  • Sojojin rundunar juyin juya hali na Iran sun bayyana shirinsu na yin yaki mai tsanani da Isra'ila da ke samun goyon bayan Amurka za su iya yakar yakin tsanani har tsawon watanni shida da Amurka da Isra’ila.
  • Firaministan Isra’ila, Benjamin Netanyahu, ya yi alkawarin ci gaba da yakin domin kawar da shugabannin Iran bayan harin haɗin gwiwa da Amurka
  • A Beirut, harin Isra’ila a wani otel ya kashe akalla mutane 4, yayin da wasu suka ji rauni, kuma hotel ɗin na daukar ‘yan gudun hijira

Abdullahi Abubakar, Editan Legit Hausa ne ta bangaren siyasa, kasuwanci da al'amuran yau da kullum, ya na da gogewar aikin jarida sama da shekaru biyar.

Tehran, Iran - Sojojin Juyin Juya Halin Iran IRGC sun yi magana kan ci gaba da yaki da ake yi tsakanin kasar da Isra'ila mai samun goyon bayan Amurka.

Rundunar ta ce a ranar Lahadi ga watan Maris, 2026 cewa ƙasar na iya yin yaki mai tsanani har tsawon watanni shida da Amurka da Isra’ila.

Kara karanta wannan

Malamin Musulunci ya fadi abin da zai faru da Isra'ila a dalilin kashe Khamenei

Iran ta razana Amurka da Isra'ila kan yakin da suke yi
Marigayi Ali Khamenei da Isra'ila ta hallaka. Hoto: @khamenei_ir.
Source: Twitter

Mai magana da yawun rundunar IRGC, Ali Mohammad Naini shi ya tabbatar da haka a cikin wata sanarwa wanda Al Jazeera ta samu.

Barazanar da Iran ta yi ga Amurka, Isra'ila

Duk da wannan barazana, Gwardiyar Juyin Juya Halin ta ce a yanzu ƙasar na iya ci gaba da “yakin tsanani” har tsawon watanni shida a wannan yanayin yaki.

Ali Mohammad Naini ya ce Iran ta yi amfani da makaman “na farko da na biyu,” amma za ta yi amfani da makaman zamani masu nisa da ba a fi amfani da su ba a kwanakin gobe.

Shugaban tsaro na Iran Ali Larijani ya zargi gwamnatin Trump da ƙoƙarin yin koyi da abin da ya faru a Venezuela inda aka kawar da shugaban Nicolás Maduro.

Ya ce:

“Sun yi tsammanin zai zama kamar Venezuela, za su kai hari, su karɓi iko kuma zai ƙare amma yanzu an makale su.”

Kara karanta wannan

Martanin malaman addini 5 game da yaƙin Iran da Isra'ila a Gabas ta Tsakiya

Shugaban hukuma mai tsauri Gholamhossein Mohseni Ejei ya kuma yi gargaɗi ga makwabtan Gabas ta Tsakiya da “a fili ko a ɓoye suna kan umarnin abokin gaba” cewa “harin tsanani kan waɗannan wurare zai ci gaba.”

Shugaban ƙasa Masoud Pezeshkian ya ce Tehran “za ta tilasta mayar da martani” idan wata ƙasa makwabta za ta yi amfani da shi a matsayin tashar kai hari ko yunkurin mamaye ƙasar.

A Beirut, harin Isra’ila a wani otel ya kashe mutane akalla 4, yayin da wasu 10 suka ji rauni.

Hotel ɗin na ɗaukar ‘yan gudun hijira daga yakin kudu da Beirut da birnin gabaɗaya, kuma wasu sun bar ginin don tsoron karin hare-hare.

Wannan shi ne karo na farko harin ya kai tsakiyar birnin tun bayan da rikicin Isra’ila da Hezbollah ya sake barkewa makon da ya gabata.

Masu nazari sun ce har yanzu babu hanyar da za a ga ƙarshen rikicin, wanda jami’an Amurka da Isra’ila ke cewa zai iya ɗaukar wata guda ko fiye.

Shugaban Amurka Donald Trump ya nuna cewa tattalin arzikin Iran zai iya sake gina idan wani shugaba “mai karɓuwa” ga Washington ya maye gurbin marigayi shugaban, amma Tehran ta ƙi wannan shawara.

Karin bayani na tafe...

Asali: Legit.ng

Authors:
Abdullahi Abubakar avatar

Abdullahi Abubakar (Hausa editor) Marubuci kuma kwararren ɗan jaridan da ya shafe shekaru 5 yana rubutu a fannin siyasa da harkokin yau da kullum. Ya kammala digirin farko a jami'ar Maiduguri. Ya samu horon aikin jarida a Reuters da AFP, ya sha halartar tarukan karawa juna sani game da bincike da adabi. Tuntube shi a abdullahi.abubakar@corp.legit.ng.