Iran Ta Kada Hantar Isra’ila, Ta Fadi Tsawon Lokacin da Za Ta Yi Tana Yakarta

Iran Ta Kada Hantar Isra’ila, Ta Fadi Tsawon Lokacin da Za Ta Yi Tana Yakarta

  • Sojojin rundunar juyin juya hali na Iran sun bayyana shirinsu na yin yaki mai tsanani da Isra'ila da ke samun goyon bayan Amurka
  • Firaministan Isra’ila, Benjamin Netanyahu, ya yi alkawarin ci gaba da yakin domin kawar da shugabannin Iran bayan harin haɗin gwiwa da Amurka
  • A Beirut, harin Isra’ila a wani otel ya kashe akalla mutane 4, yayin da wasu suka ji rauni, kuma hotel ɗin na daukar ‘yan gudun hijira

Abdullahi Abubakar, Editan Legit Hausa ne ta bangaren siyasa, kasuwanci da al'amuran yau da kullum, ya na da gogewar aikin jarida sama da shekaru biyar.

Tehran, Iran - Sojojin Juyin Juya Halin Iran, IRGC sun yi magana kan ci gaba da yaki da ake yi tsakanin kasar da Isra'ila mai samun goyon bayan Amurka.

Rundunar ta ce a ranar Lahadi 8 ga watan Maris, 2026 ƙasar na iya yin yaki mai tsanani har tsawon watanni shida da Amurka da Isra’ila.

Kara karanta wannan

Malamin Musulunci ya fadi abin da zai faru da Isra'ila a dalilin kashe Khamenei

Iran ta razana Amurka da Isra'ila kan yakin da suke yi
Marigayi Ali Khamenei da Isra'ila ta hallaka. Hoto: @khamenei_ir.
Source: Twitter

Mai magana da yawun rundunar IRGC, Ali Mohammad Naini shi ya tabbatar da haka a cikin wata sanarwa wanda Al Jazeera ta samu.

Barazanar da Iran ta yi ga Amurka, Isra'ila

Duk da wannan barazana, Gwardiyar Juyin Juya Halin ta ce a yanzu ƙasar na iya ci gaba da “yaki mai tsanani” har tsawon watanni shida a wannan yanayin.

Ali Mohammad Naini ya ce Iran ta yi amfani da makaman “farko da na biyu,” amma za ta yi amfani da makaman zamani masu nisa da ba a fi amfani da su ba a gaba.

Shugaban tsaro na Iran Ali Larijani ya zargi gwamnatin Trump da ƙoƙarin yin koyi da abin da ya faru a Venezuela inda aka kawar da shugaban Nicolás Maduro.

Ya ce:

“Sun yi tsammanin zai zama kamar Venezuela, za su kai hari, su karɓi iko kuma zai ƙare amma yanzu an makale su.”

Kara karanta wannan

Martanin malaman addini 5 game da yaƙin Iran da Isra'ila a Gabas ta Tsakiya

Iran ta gargadi Amurka da Isra'ila a Gabas ta Tsakiya
Marigayi jagoran Musulunci a Iran, Ali Khamenei. Hoto: @khamenei_ir.
Source: Twitter

Gargadin da Iran ta yi ga kasashen Larabawa

Shugaban hukuma mai tsauri Gholamhossein Mohseni Ejei ya kuma yi gargaɗi ga makwabtansu “a fili ko a ɓoye da ke bin umarnin abokin gaba” cewa “hari mai tsanani kan waɗannan wurare zai ci gaba.”

Shugaban ƙasa Masoud Pezeshkian ya ce Tehran “za ta tilasta mayar da martani” idan wata ƙasa makwabta za ta yi amfani da shi a matsayin tashar kai hari ko yunkurin mamaye ƙasar.

A Beirut, harin Isra’ila a wani otel ya kashe mutane akalla 4, yayin da wasu 10 suka ji rauni, cewar rahoton Times of Israel.

Hotel ɗin na ɗaukar ‘yan gudun hijira daga yakin kudu da Beirut da birnin gaba ɗaya, kuma wasu sun bar ginin don tsoron karin hare-hare.

Wannan shi ne karo na farko harin ya kai tsakiyar birnin tun bayan da rikicin Isra’ila da Iran ya sake barkewa makon da ya gabata.

Kara karanta wannan

Rasha ta fadi dalilin da ya sa ba ta kai dauki ga Iran ba a yakinta da Isra'ila

Matan gwamnatin Najeriya kan yakin Iran/Isra'ila

An ji cewa Gwamnatin tarayyar Najeriya ta yi magana game da matakan da take dauka kan yakin da ke faruwa tsakanin kasar Iran da Isra'ila.

Gwamnatin ta bayyana cewa tana yin haka ne domin kare ‘yan Najeriya da ke Gabas ta Tsakiya sakamakon rikicin da ake yi a yau.

Ma’aikatar harkokin waje ta ce jakadun Najeriya a ƙasashen yankin an saka su cikin shiri na musamman domin sa ido kan halin da ake ciki.

Asali: Legit.ng

Authors:
Abdullahi Abubakar avatar

Abdullahi Abubakar (Hausa editor) Marubuci kuma kwararren ɗan jaridan da ya shafe shekaru 5 yana rubutu a fannin siyasa da harkokin yau da kullum. Ya kammala digirin farko a jami'ar Maiduguri. Ya samu horon aikin jarida a Reuters da AFP, ya sha halartar tarukan karawa juna sani game da bincike da adabi. Tuntube shi a abdullahi.abubakar@corp.legit.ng.