Akwai Matsala: Majalisar Dinkin Duniya Ta Hango Abin da Zai Faru sakamakon Yakin Amurka da Iran
- Shugaban Majalisar Dinkin Duniya, António Guterres ya bukaci Amurka, Isra'ila da Iran su tsagaita wuta, su koma teburin tattaunawa
- Guterres ya ce matukar ba a gaggauta magance yakin da ya barke a Gabas ta Tsakiya ba, to zai iya kai wa matakin da zai fi karfin kowa
- Kasar Iran dai ta sha nanata cewa ba ta neman yaki da rikici da kowa, amma za ta dauki duk matakin da ya dace domin kare 'yancinta
CHECK OUT: How to Start Earning with Copywriting in Just 7 Days – Even if You’re a Complete Beginner
Ahmad Yusuf, kwararren edita ne a Legit Hausa da ya shafe tsawon shekaru yana kawo muku rahotannin siyasa, nishadi da al'amuran yau da kullum
America - Shugaban Majalisar Dinkin Duniya, António Guterres, ya yi gargaɗin cewa rikicin da ke faruwa a yankin Gabas ta Tsakiya na iya rikidewa ya fi karfin kowa idan ba a dauki mataki ba.
Wannan gargadi na zuwa ne yayin da yaki ke kara zafi tsakanin hadin gwiwar Amurka da Isra'ila da kuma Jamhuriyar Musulunci ta Iran.

Source: Getty Images
Premium Times ta ce a cikin wata sanarwa, Guterres ya ce hare-haren da ake kai wa juna a yankin da ma sauran wurare na haifar da babbar matsala ga fararen hula, tare da haddasa mummunar illa.
Abin da rikin Iran da Amurka zai haifar
Ya kuma yi gargadin cewa rikicin na iya haifar da babbar barazana ga tattalin arzikin duniya, musamman ga mutanen da suka fi rauni a ƙasashe masu tasowa.
“Lamarin na iya rikidewa ya fi karfin kowa. Lokaci ya yi da za a dakatar da faɗa kuma a koma kan teburin tattaunawar diflomasiyya,” in ji Guterres.
A halin yanzu dai ana ci gaba da musayar wuta tsakanin Amurka, Isra'ila da Iran. Rikicin ya shiga rana ta takwas a yau Asabar, kamar yadda France 24 ta rahoto.
Babban jami’in kula da ayyukan agajin gaggawa na Majalisar Ɗinkin Duniya, Tom Fletcher, ya ce duniya na cikin wani mawuyacin lokaci, wanda ke nuna hadarin da ke tunkarowa.

Kara karanta wannan
Kasar Iran ta farmaki wani jirgin yaki, ta kara yi wa Amurka da Isra'ila babbar illa
Ya bayyana damuwa kan yadda ake kashe kuɗaɗe masu yawa wajen yaƙi, yayin da a lokaci guda wasu ‘yan siyasa ke zaftare kuɗin agaji ga mutanen da suka fi buƙata.
Yadda yakin Iran zai lalata harkokin jin kai
Hukumar kare haƙƙin ɗan Adam ta Majalisar Ɗinkin Duniya, ƙarƙashin jagorancin Volker Türk, ta ayyana rikicin a matsayin babbar matsala ga harkokin jin ƙai, wacce ke buƙatar a magance ta cikin gaggawa.
Türk ya yi gargaɗin cewa rikicin na ci gaba da yaɗuwa zuwa wasu kasashe fiye da waɗanda suka fara musayar wutan tun farko, yana mai kira ga ƙasashe su ɗauki matakan rage tashin hankali.

Source: Getty Images
A nasa ɓangaren, wakilin Iran a Majalisar Ɗinkin Duniya, Amir Iravani, ya ce ƙasarsa ba ta neman yaƙi ko ƙara tsananta rikici, amma ba za ta taɓa miƙa wuya ga duk wani hari kan ikon ƙasarta ba.
Trump ya gindaya sharadin zaman lafiya da Iran
A wani rahoton, kun ji cewa Shugaba Donald Trump na kasar Amurka ya bayyana cewa mika wuyan Iran ba tare da sharadi ba ne kadai zai kawo karshen yakin da ya barke.
Wannan furuci na Trump ya zo ne a lokacin da Isra’ila ke ci gaba da kai hare-hare kan wuraren gwamnati a birnin Tehran na Iran.
Trump ya ƙara da cewa idan Iran ta amince da wannan sharadi na mika wuya, Amurka da ƙawayenta za su taimaka wajen farfaɗo da tattalin arzikin ƙasar.
Wanda ya tantance Muhammad Malumfashi, babban edita a Legit.ng.
Asali: Legit.ng
