Wata Sabuwa: Shugaban Amurka Ya Kawo Tarnaki a Shirin Nada Sabon Jagoran Addinin Iran

Wata Sabuwa: Shugaban Amurka Ya Kawo Tarnaki a Shirin Nada Sabon Jagoran Addinin Iran

  • Shugaban Amurka, Donald Trump na neman kawo hargitsi a shirin Iran na nada sabon jagora, wanda zai gaji Ayatollah Ali Khamenei
  • A wata hira da aka yi da shi yau Alhamis, Trump ya bayyana cewa ya kamata a sanya shi a cikin wadanda za su zabi sabon jagoran Iran
  • Ya kara da cewa ya samu labarin ana shirin nada dan marigayi, Mojtaba Khamenei, inda ya ce ba zai yarda da wannan zabi ba

Ahmad Yusuf, kwararren edita ne a Legit Hausa da ya shafe tsawon shekaru yana kawo muku rahotannin siyasa, nishadi da al'amuran yau da kullum

Amurka - Shugaba Donald Trump na neman a sanya shi a cikin wadanda za su zabi sabon jagoran addini na Jamhuriyar Musulunci ta Iran.

Wannan na zuwa ne yayin da Iran ke ci gaba da shirye-shiryen nada sabon jagora bayan kashe Ayatollah Ali Khamenei a hare-haren hadin gwiwar Amurka da Isra'ila.

Kara karanta wannan

Khamenei: An ɗage taron jana'izar jagoran addini a Iran yayin da ake harin magajinsa

Shugaba Trump.
Shugaban kasar Amurka, Donald Trump a fadar White House Hoto: Win Mcnamee
Source: Getty Images

Trump na neman shiga harkokin Iran

Tashar Al-Jazeera ta ruwaito cewa Shugaba Donald Trump, ya bayyana cewa yana ganin ya kamata a ba shi damar shiga cikin zaɓen sabon jagoran Iran bayan rasuwar Khamenei.

Har yanzu dai Iran ba ta nada jagoran addini na kasar ba, amma rahotanni daga birnin Tehran sun nuna cewa dan marigayi, Mojtaba Khamenei ne a sahun gaba cikin wadanda ake ganin za su karbi ragamar kasar.

A wata hira da ya yi da kafar watsa labarai ta Axios, Trump ya ce Iran na “ɓata lokacinta” idan ta yi ƙoƙarin naɗa sabon jagora ba tare da sa hannun Amurka ba.

Trump ya yi fatali da shirin nada 'dan Khamenei

Shugaba Trump ya ce ya samu labarin cewa Mojtaba Khamenei, ɗan marigayi Ali Khamenei, shi ne wanda ake ganin zai iya gadon mahaifinsa a matsayin sabon jagoran Iran. Sai dai ya ce ba zai amince da hakan ba.

Kara karanta wannan

Yaki na kara zafi da Amurka, an ji shirin da Iran take yi na nada magajin Ayatollah Khamenei

“Ɗan Khamenei ba shi da ƙarfi, dole ne ni ma in kasance cikin waɗanda za su zaɓi sabon jagoran Iran," in ji Trump.

Wanda Amurka take son Iran ta nada

Ya ƙara da cewa duk wanda za a naɗa a matsayin sabon jagoran Iran idan ya ci gaba da manufofin tsohon shugabanci, hakan na iya janyo sabon rikici da Amurka nan da shekaru biyar.

Trump ya kuma jaddada cewa:

“Ɗan Khamenei ba abin karɓa ba ne a gare ni. Muna son wanda zai kawo zaman lafiya da haɗin kai a Iran.”

Wannan kalamai na Trump na zuwa ne bayan shiga rana ta 6 da fara yaki tsakanin Amurka/Isra'ila da Iran, wanda kawo yanzu ya jawo asarar rayukan mutane fiye da 1000.

Khamenei.
Tsohon jagoran addinin Iran da ya rasa ransa a harin Amurka, Ayatollah Ali Khamenei Hoto: Masoud
Source: Getty Images

Tsohon sojan Amurka ta tada hayaniya a Majalisa

A wani rahoton, kun ji cewa wani tsohon sojan Amurka ya tayar da bore yayin zaman wani kwamitin majalisar dattawa kan batun yakin da kasar ta shiga da Iran.

Tsohon soojan, wanda aka ruwaito ya taba takarar sanata, ya tada hayaniya tare da katse zaman da ake yi a Capitol Hill domin nuna rashin amincewa da yaƙin Amurka da Isra’ila da ƙasar Iran.

Kara karanta wannan

Ana tsakiyar musayar wuta, Iran ta yi maganar sulhu da Amurka a rana ta 5

Sanata Tim Sheehy na jam'iyyar Republican daga jihar Montana, ya taimaka wa jami'an 'yan sanda da dama wajen fitar da mutumin.

Asali: Legit.ng

Authors:
Ahmad Yusuf avatar

Ahmad Yusuf (Hausa editor) Ahmad Yusuf ma'aikacin jaridar Legit.ng sashin Hausa ya fara aiki a 2021, ya kware wajen kawo labarai da rahotanni da suka shafi siyasa da al'amuran yau da kullum. Matashin ɗan jaridar ya koyi Lissafi a digirinsa na farko a Jami'ar Kimiyya da Fasaha da ke Wudil, Kano (KUST) ya kuma samu shaidar kwarewa a fannin aikin jaridar zamani daga Reuters a 2022. Kafin fara aiki da Legit Ahmad ya yi aiki da jaridu da dama na turanci da Hausa tun 2012. Mail: ahmad.yusuf@corp.legit.ng 07032379262