Najeriya Ta Shiga Jerin Kasashe 3 da Za Su Samu Alheri sakamakon Yakin Iran da Amurka

Najeriya Ta Shiga Jerin Kasashe 3 da Za Su Samu Alheri sakamakon Yakin Iran da Amurka

  • Rahoto ya nuna cewa duk da yakin Iran da Amurka/Isra'ila ba alheri ba ne ga tattalin arzikin duniya, amma wasu kasashen Afirka za su amfana
  • A wani bincike da aka yi, Najeriya na daga cikin kasashen da lalitarsu za ta yi kauri saboda karuwar kudade shiga sakamakon tsadar gangar mai
  • Sai dai binciken ya nuna cewa galibin kasashen nahiyar Afirka za su shiga matsin tattalin arziki ne sakamakon yakin da ake yi a Gabas ta Tsakiya

Ahmad Yusuf, kwararren edita ne a Legit Hausa da ya shafe tsawon shekaru yana kawo muku rahotannin siyasa, nishadi da al'amuran yau da kullum

Abuja, Nigeria - Rahotanni sun nuna cewa tashin farashin danyen mai a kasuwannin duniya sakamakon yakin Amurka, Isra'ila da Iran zai amfani tattalin arzikin wasu kasashe.

Wannan na zuwa ne yayin da musayar wuta ke kara zafi a tsakanin kasashen, tun bayan barkewar yaki da safiyar ranar Asabar, 28 ga watan Fabrairun 2026.

Kara karanta wannan

Yakin Amurka da Iran: Matatar Dangote ta yi magana kan yiwuwar samun man fetur a Najeriya

Tinubu da gangar mai.
Shugaban kasa, Bola Ahmed Tinubu da gangar danyen mai Hoto: @aonanuga1956, Bloomberg
Source: Getty Images

Jaridar The Cable ta tattaro cewa wannan yaki da ba shi da alamun karewa nan kusa, ya jawo tashin farashin gangar danyen mai a kasuwannin duniya.

Najeriya za ta samu karin kudin shiga

A cewar wani rahoto da Bloomberg Economics ta fitar ranar Alhamis, kasashen uku kacal a yankin Afrika ta kudu da Sahara za su samu karin kudaden shiga sakamakon wannan yaki.

Rahoton ya ce kasshen Angola, Nigeria da Ghana ne tattalin arzikinsu zai bunkasa ta fuskar kudaden shiga sakamakon tashin farashin mai.

Sai dai rahoton ya bayyana cewa yawancin sauran kasashen yankin za su fuskanci matsin tattalin arziki ne saboda yakin.

Tasirin karin farashin mai ga Afirka

Wata masaniyar harkokin tattalin arziki ta jairdar, Yvonne Mhango, ta ce idan farashin danyen mai ya tsaya a $85 a kowace ganga, kasashen Angola, Najeriya da Ghana za su samu sauki a bangaren hada-hadar kasuwanci da kasashen waje.

Kara karanta wannan

Aminu Gwarzo: Matakai 8 da majalisar Kano za ta bi don tsige mataimakin gwamna

Sai dai ta ce kasashe kamar Jamhuriyar Dimokuradiyyar Congo, Afirka ta Kudu da Kenya za su fi shan wahala.

Ta kara da cewa mafi yawan kasashen Afirka za su iya fuskantar raguwar darajar kudinsu, karuwar hauhawar farashi da yiwuwar bankunan kasa su kara kudin ruwa.

Najeriya na iya cin gajiyar tsadar danyen mai

Rahoton ya bayyana cewa Angola na iya kara samun kusan kashi 3.3% na GDP daga karin farashin mai, yayin da Nigeria za ta amfana ba kawai daga sayar da danyen mai ba, har ma daga fitar da man fetur da aka tace.

A cikin rahoton, an ambaci attajirin Najeriya Aliko Dangote, wanda ya ce matatar man da ya gina mai karfin tace ganga 650,000 a rana na iya fara fitar da man fetur zuwa kasashen Turai idan farashin ya yi kyau.

Rahoton ya nuna cewa farashin gangar danyen mai na Brent crude ya tashi zuwa Dala 85 a ranar 3 ga Maris, daga dala 72 da ake sayarwa a ranar 28 ga Fabrairu, 2025.

Kara karanta wannan

Malamai sun yi magana, sun fadi yadda yakin Iran da Amurka ya shafi Najeriya

Gangunan mai.
Gangunan danyen mai da ake hada-hada a kasuwannin duniya Hoto: GAIZKA IROZ
Source: Getty Images

Litar fetur ta kara tsada a Najeriya

A wani rahoton, kun ji cewa yakin Iran da Amurka/Isra'ila ya fara shafar yan Najeriya yayin da aka ruwaito cewa farashin litar fetur ta kara tashi a gidajen mai.

Bayan tashin farashin danyen mai a kasuwar duniya, matatar mai ta Dangote , a ranar Litinin, ta kara N100 kan kowane lita, inda ta mayar da farashin sari daga N774 zuwa N874.

Sakamakon haka, gidajen mai a fadin kasar nan suka fara sauya nasu farashin litar fetur, lamarin da zai shafi talakawan Najeriya kai tsaye.

Wanda ya tantance Muhammad Malumfashi, babban edita a Legit.ng.

Asali: Legit.ng

Authors:
Ahmad Yusuf avatar

Ahmad Yusuf (Hausa editor) Ahmad Yusuf ma'aikacin jaridar Legit.ng sashin Hausa ya fara aiki a 2021, ya kware wajen kawo labarai da rahotanni da suka shafi siyasa da al'amuran yau da kullum. Matashin ɗan jaridar ya koyi Lissafi a digirinsa na farko a Jami'ar Kimiyya da Fasaha da ke Wudil, Kano (KUST) ya kuma samu shaidar kwarewa a fannin aikin jaridar zamani daga Reuters a 2022. Kafin fara aiki da Legit Ahmad ya yi aiki da jaridu da dama na turanci da Hausa tun 2012. Mail: ahmad.yusuf@corp.legit.ng 07032379262