Iran Ta Ce Ta Kashe Sojojin Amurka 500 a Luguden Wuta da Ta Masu

Iran Ta Ce Ta Kashe Sojojin Amurka 500 a Luguden Wuta da Ta Masu

  • Kasar Iran ta ce ta kashe sojojin Amurka a kalla 500 bayan shafe kwana biyar suna gwabza yakin da ya shafi yawancin kasashen Gabas ta Tsakiya
  • Babban jami'in gwamnatin Iran, Ali Larijani ne ya bayyana haka, inda ya ce za su cigaba da fafatawa da Amurka/Isra'ila kan harin da suka kai masu
  • Iran ta fitar da bayanin ne a daidai lokacin da shugaba Donald Trump ke ikirarin cewa yana samun nasara a hadin gwiwar da ya ke da Isra'ila a yakin

Editan Legit Hausa Ibrahim Yusuf yana da gogewar aikin jarida da rubuce-rubucen adabi sama da shekaru hudu, kuma kwararre ne a kawo rahotannin kasuwanci, siyasa da lamuran yau da kullum.

Iran - Yayin da Amurka ke ikirarin cewa tana samun nasara a yakin da take yi da Iran, Tehran ya sanar da cewa ya kashe sojojin Washington akalla 500.

Ikirarin ya zo ne duk da cewa gwamnatin Trump ta nuna hotunan sojoji hudu da suka mutu a rikicin da ke tsakanin Amurka da Isra’ila da Iran, wanda ya shiga rana ta biyar a ranar Laraba.

Kara karanta wannan

Komai ya fito: An fadi aikin da sojojin Amurka da aka jibge a Bauchi za su yi

Ali Larijani yana wani bayani
Daya daga cikin manyan jami'an Iran, Ali Larijani. Hoto: @alilarijani_ir
Source: Twitter

Iran ta kashe sojojin Amurka 500

Daya daga cikin manyan jami’an tsaron kasar Iran, Ali Larijani, ya yi ikirari a X cewa sun kashe sojojin Amurka 500 a ‘yan kwanakin da suka gabata.

A cikin wani sako da ya wallafa, Larijani ya ce:

“Trump da ya fada tarkon Benjamin Netanyahu, ya jefa al’ummar Amurka cikin wani yaki marar tsari da Iran.
"Ya kamata ya yi lissafi yanzu, idan sama da sojojin Amurka 500 sun mutu cikin ‘yan kwanakin nan, shin har yanzu Amurka yake karewa ko Isra’ila?”

Lajarani ya kuma kara da cewa lamarin bai kare ba, kuma kashe Imam Khamenei ba zai tafi a banza ba, inda ya ce za su dauki fansa.

Maganar Trump kan mutuwar sojojin Amurka

Yayin da ya ke magana kan kashe sojojin Amurka hudu da aka yi a farkon yakin, Shugaba Donald Trump ya bayyana cewa za a iya samun karin mutuwar dakaru a fafatawar da ke.

Kara karanta wannan

Kanada ta gano masu laifi a yakin da ya barke tsakanin Amurka, Isra'ila da Iran

NDTV ta rahoto ya ce:

“Abin takaici ne, kuma akwai yiwuwar karin mutuwa kafin yakin ya kare. Haka abin yake.”

Wane ne Ali Larijani a kasar Iran?

Ali Larijani yana daga cikin manyan masu tasiri a siyasar Iran, na daga cikin ‘yan tsirarun mutanen da marigayi Ayatollah Ali Khamenei ya amince da su wajen tabbatar da dorewar tsarin mulkin kasar.

Bayan sa'o'i 24 kacal da fara hare-haren Amurka da Isra’ila a kan Tehran, Larijani ya bayyana a talabijin kasar da kafafen sada zumunta inda ya zargi Amurka da Isra’ila da kai harin.

Ya ce:

“Za mu kona zukatansu. Amurkawa marasa kunya za su yi nadamar abin da suka aikata.”
Jagoran addinin Iran da aka kashe
Ayatollah Ali Khamenei da aka kashe a Iran. Hoto: Getty Images
Source: Twitter

A tsawon rayuwarsa ta siyasa wadda ta dauki sama da shekaru 10, Larijani yana da tasiri a tsarin mulkin Iran, kuma gogaggen mai tattaunawa ne da kasashe irin su Rasha, China har ma da Amurka.

Mojtaba Khamenei na raye

A wani labarin, kun ji cewa wasu majiyoyi sun tabbatar da cewa dan marigayi Ayatollah Ali Khamenei mai suna Mojtaba yana nan da rai.

Kara karanta wannan

Yakin Amurka/Isra'ila da Iran: Muhimman abubuwan da suka faru a rana ta 5

Iran ta sanar da cewa Mojtaba na raye yayin da aka fara rade-radin cewa ya mutu a harin da Amurka/Isra'ila suka kai gidansu.

An fara hasashen cewa zai iya maye gurbin mahaifinsa a matsayin sabon jagoran Iran, lamarin da ya sa hankula komawa kansa.

Wanda ya tantance Muhammad Malumfashi, babban edita a Legit.ng.

Asali: Legit.ng

Authors:
Ibrahim Yusuf avatar

Ibrahim Yusuf (Hausa Editor) Ibrahim Yusuf yana da gogewar aikin jarida da rubuce-rubucen adabi sama da shekaru hudu, kuma kwararre ne a kawo rahotannin kasuwanci, siyasa da lamuran yau da kullum. ibrahim.yusuf@corp.legit.ng