An Samu Matsala: Amurka Ta Yi Wa Iran Babbar Illa a cikin Teku

An Samu Matsala: Amurka Ta Yi Wa Iran Babbar Illa a cikin Teku

  • Ana ci gaba da fafata yaki mai zafi bayan Amurka da Isra'ila sun kaddamar da hare-hare ta sama kan kasar Iran a yankin Gabas ta tsakiya
  • Wani jirgin ruwan yaki na kasar Amurka da ke tafiya a karkashin ruwa ya harba makami mai hadari kan jirgin ruwan yaki na Iran a cikin teku
  • Mahukunta sun bayyana cewa an tura masu aikin ceto bayan samun kiran neman daukin gaggawa daga jirgin ruwan da aka harbawa makamin

​​​​​​​​Editan Legit Hausa Sharif Lawal yana da kwarewar shekaru wajen kawo rahotannin siyasa, al'amuran yau da kullum, tsegumi da nishadi

Kasar Iran - Wani jirgin ruwan yaƙi na ƙasar Amurka wanda ke tafiya a ƙarƙashin ruwa ya harba makamin torpedo kan jirgin ruwan yakin Iran.

Makamin da aka harba ya nutsar da jirgin ruwan yaƙin Iran a ruwan ƙasa da ƙasa da ke kusa da gaɓar tekun Sri Lanka.

Amurka ta nutsar da jirgin ruwan yakin Iran
Shugaba Donald Trump na Amurka da jirgin ruwan yaki Hoto: @Osinttechnicalx, @jurgen_nauditt
Source: Twitter

Tashar Aljazeera ta kawo rahoton cewa Ministan tsaro na Amurka, Pete Hegseth, ya bayyana hakan yayin ganawa da manema labarai a ranar Laraba, 4 ga watan Maris 2026.

Kara karanta wannan

Ana tsakiyar musayar wuta, Iran ta yi maganar sulhu da Amurka a rana ta 5

Pete Hegseth ya bayyana cewa wannan harin da aka kai wa jirgin ruwan yaƙin na Iran shi ne irin hari na farko da aka kai wa maƙiyi tun bayan yaƙin duniya na biyu.

Shafin @DeptofWar a X ya sanya bidiyon yadda aka harba makamin da ya nutsar da jirgin ruwan yakin na Iran.

An samu asarar rayuka

Gwamnatin Sri Lanka ta bayyana cewa ta gano gawarwaki da dama sannan ta ceto sojojin ruwa 32 da suka jikkata bayan da jirgin yaƙin na Iran ya nutse a daidai wajen iyakokin ruwan tsibirin.

Mataimakin ministan harkokin wajen ƙasar ya bayyana cewa aƙalla mutane 80 ne aka kashe a wannan harin.

Hukumomi sun bayyana cewa jirgin ruwan yaƙin mai suna IRIS Dena, wanda ke nisan kusan mil 40 (kilomita 75) daga Galle a Kudancin Sri Lanka, ya aika da saƙon neman ɗauki tsakanin ƙarfe 6:00 na safe zuwa 7:00 na safe a ranar Laraba.

Jirgin ruwan yakin Iran na dauke da mutane

Jirgin yana ɗauke da kimanin ma’aikata 180 a cikinsa, kuma ana ci gaba da gudanar da aikin neman mutane da ceton rayuka, in ji jami’an Sri Lanka.

Kara karanta wannan

Luguden wutar Iran ya jefa Amurkawa cikin tsoro, suna korafi ga Trump

Ministan harkokin wajen Sri Lanka, Vijitha Herath, ya shaida wa majalisar dokoki cewa rundunar sojojin ruwa ta samu labarin cewa jirgin yana cikin mawuyacin hali, kuma gwamnati ta aika da jiragen ruwa da na rundunar sojojin sama domin aikin ceto.

Kakakin rundunar sojojin ruwan Sri Lanka ya ce ba a ga wani jirgin ruwa ko na sama a yankin da jirgin yaƙin na Iran ya nutse ba a lokacin da abin ya faru.

Amurka ta nutsar da wani jirgin ruwan yakin Iran
Jirgin ruwan yakin Iran a cikin teku Hoto: @mario_naufal
Source: Twitter

Ana gwabza fada tsakanin Amurka da Iran

Nutsar da jirgin ruwan yaƙin ya faru ne a daidai lokacin da Amurka da Isra’ila ke ci gaba da kai hare-hare ta sama kan Iran har tsawon kwanaki biyar, bayan kashe Ali Khamenei da wasu mutane kusan 800, ciki har da ɗumbin ɗalibai mata.

Iran ta mayar da martani da hare-haren jirage marasa matuƙi da makamai masu linzami kan Isra’ila da sansanonin sojojin Amurka a ƙasashen Gabas ta Tsakiya, wanda ya yi sanadiyar mace-mace da dama.

Sojojin Amurka shida ne aka kashe yayin da wasu da dama suka jikkata.

Amurka ta yi asara a yaki da Iran

A wani labarin kuma, kun ji cewa kasar Amurka ta tafka asara bayan fara yakin da ta yi da Iran tare da hadin gwiwar Isra'ila.

Kara karanta wannan

Amurka ta gamu da gagarumar matsala a yaki da Iran, Spain ta juya wa Trump baya

Amurka ta yi asarar kusan Dala biliyan biyu na kayan aikin soja tun bayan da rikici ya barke tsakaninta da Iran.

Hare-haren ramuwar gayya da Iran ta kaddamar sun janyo babbar asara ga kadarorin sojojon Amurka a yankin Gabas ta Tsakiya.

Wanda ya tantance Muhammad Malumfashi, babban edita a Legit.ng.

Asali: Legit.ng

Authors:
Sharif Lawal avatar

Sharif Lawal (Hausa Editor) Sharif Lawal ma'aikacin jarida ne wanda ya samu gogewa a harkar aikin jarida. Ya yi digirinsa na farko a jami'ar Ahmadu Bello (ABU) da ke Zaria. Ya samu horo daga Reuters kan aikin jarida da tantance labarai. Za a iya tuntubarsa ta Sharif.lawal@corp.legit.ng