Jirgin Sama Dauke da Makudan Kudi Ya Gamu da Hatsari, Mutane Sun Daka Wawa
- Wani jirgin sama na dakon kaya mallakin rundunar sojojin Bolivia ya yi hatsari a kusa da babban birnin kasar, La Paz
- Rahotanni sun nuna jirgin ya dauko takardun kudi masu yawa lokacin da ya rikito kan titi, an tabbatar da mutuwar mutane 20
- Gwamnatin Bolivia ta gargadi mazauna yankin da aka ce sun daka wawa kan kudin da jirgin ya dauko, ta ce amfani da su babban laifi ne
Legit.ng Hausa ta bude tasha a manhajar Whatsapp. Kasance tare da mu don samun rahotanni da dumi-dumi!
Ahmad Yusuf, kwararren edita ne a Legit Hausa da ya shafe tsawon shekaru yana kawo muku rahotannin siyasa, nishadi da al'amuran yau da kullum
Bolivia - Akalla mutane 20 ne suka riga mu gidan gaskiya sa'ilin da wani jirgin jigilar kayayyaki na sojin ƙasar Bolivia, wanda ke ɗauke da takardun kuɗi, ya yi hatsari.
Jirgin saman, wanda ke dauke da makudan kudi, ya gamu da hatsari ne yayin da yake ƙoƙarin sauka kusa da babban birnin ƙasar, La Paz.

Source: Getty Images
Jirgin sama dauke da kudi ya yi hatsari
Rundunar 'yan sanda ta sanar da hakan a ranar Juma'a, yayin da cincirindon jama'a suka yi ƙoƙarin kwashe kuɗaɗen da suka watsu, kamar yadda tashar Channels ta kawo.
Jirgin, samfurin C-130 Hercules wanda kamfanin Lockheed Martin ya kera, ya kauce hanyarsa ne a filin jirgin sama na El Alto, inda ya faɗa kan wani babban titi, ya murƙushe motoci da dama.
Jama'a sun daka wa kudi wawa a Bolivia
An ga baraguzan jirgin a kan titin da ya faɗa, sannan an hango mutane na rugawa domin kwashe tsabar kuɗin da suka watsu, lamarin da ya sa 'yan sanda harba barkonon tsohuwa domin tarwatsa su
Jaridar The Times of India ta dauko rahoton cewa daga bisani, an hango jami'ai suna cinna wa kuɗaɗen wuta a wurin da hatsarin ya afku.
Har yanzu ba a tantance musabbabin hatsarin ba, amma shaidu sun shaida cewa yanayin sararin samaniya ya kasance mai matuƙar haɗari.
"Akwai ƙanƙara mai ƙarfi tana fadowa kuma ana yin walƙiya” lokacin da jirgin ya faɗo, in ji Cristina Choque, wata mai sayar da kaya 'yar shekara 60 wacce fallen jirgin ya faɗa wa motarta.
An tabbatar da mutuwar mutane 20
Ma'aikatar Tsaron ƙasar ta ce za ta ƙaddamar da bincike kan hatsarin. Kwamandan 'yan sanda mai kula da sashin binciken kisan kai a El Alto, Colonel Rene Tambo, ya shaida wa manema labarai cewa an yi asarar rayuka "kusan 20, ko ma fiye da haka."
Ma'aikatar Lafiya ta Bolivia ta bayar da rahoton cewa akalla mutane 28 ne suka ji rauni, wadanda yanzu haka suke karbar magani.

Source: Getty Images
A cikin wata sanarwa, ma'aikatar tsaron ta bayyana cewa:
“Kuɗaɗen da jirgin ke ɗauke da su ba su da lambar shaida ta hukuma saboda haka ba za a iya amfani da su ba a doka. Tarawa, mallaka, ko amfani da su babban laifi ne.”
Karamin jirgin sama ya fado titi a Georgia
A wani rahoton, kun ji cewa wani matuki da dalibinsa sun tsira daga mutuwa bayan karamin jirginsu ya yi hatsari a kan babbar hanya a jihar Georgia.

Kara karanta wannan
Tashin hankali: 'Yan Boko Haram sun farmaki karamar hukumar gwamna ana cikin Ramadan
Rahotanni daban-daban sun nuna cewa jirgin ya fuskanci matsalar inji ne jim kaɗan bayan ya tashi daga filin tashi da sauka na Lee Gilmer Memorial.
Matukin jirgin Thomas Rogers ya yi ban kwana da iyalinsa ta hanyar aika sakon murya bayan ya fahimci cewa injin jirgin ya daina aiki.
Wanda ya tantance Muhammad Malumfashi, babban edita a Legit.ng.
Asali: Legit.ng

