Rikici Ya Barke a Zauren Majalisa, An Yi Yunkurin Hana Rantsar da Sabon Minista
- Shugaba Tayyip Erdogan ya nada Akin Gurlek a matsayin ministan shari'a na Turkiyya duk da kakkausan sukan da jam'iyyar adawa take yi
- Rikici ya barke a majalisar dokokin Turkiyya yayin rantsar da sabon ministan inda aka ga sanatoci suna dambe a kokarin hana rantsuwar
- Wani bidiyo ya nuna yadda ‘yan majalisar CHP suka yi yunƙurin toshe Gurlek, inda aka ga ana ture juna da kai naushi tsakanin sanatoci
CHECK OUT: How to Start Earning with Copywriting in Just 7 Days – Even if You’re a Complete Beginner
Istanbul - Shugaban ƙasar Turkiyya, Tayyip Erdogan, ya naɗa babban mai shigar da ƙara na Istanbul, Akin Gurlek, a matsayin sabon ministan shari’a, wanda hakan ya haddasa kakkausan suka.
Gurlek ne mutumin da ya jagoranci kaddamar da bincike da kama mambobin babbar jam’iyyar adawa ta CHP tun bayan naɗa shi a shekarar 2024.

Source: Getty Images
Tabon da ke jikin sabon ministan Turkiyya
Wannan naɗi ya harzuka jam’iyyar adawa, inda suke ganin matakin a matsayin wani farmaki ne ga tsarin dimokuradiyya da kuma bin doka da oda a ƙasar, in ji rahoton Reuters.
Akin Gurlek ne ya jagoranci binciken da ya kai ga kama Ekrem Imamoglu, magajin garin Istanbul kuma babban abokin hamayyar Erdogan, wanda ke garkame tun watan Maris na 2025.
A cikin wani kundin tuhuma mai shafuka 4,000 da ya gabatar a watan Nuwamban da ya gabata, Gurlek ya buƙaci a ɗaure Imamoglu na tsawon shekaru sama da 2,000.
Wannan tuhuma, wadda ta shafi zargin jagorantar gungun masu cin hanci da rashawa, ta janyo gagarumar zanga-zanga a titunan Turkiyya wadda ba a taɓa ganin irinta ba cikin shekaru 10.
Ana sa ran za a gudanar da zaman sauraron ƙarar na farko a watan gobe, inda ake tuhumar ɗaruruwan mutane da ke da alaƙa da hukumar birnin Istanbul.
Hargitsi da kokowa a majalisar Turkiyya
An samu barkewar hayaniya da dambe a majalisar dokokin Turkiyya gabanin rantsar da Gurlek, yayin da ‘yan majalisar adawa suka nuna rashin amincewarsu da nadinsa.
Kamar yadda hotunan talabijin suka nuna, ‘yan majalisar jam’iyyar CHP sun yi yunƙurin toshe Gurlek, inda aka ga ana ture juna da kai naushi tsakanin sanatoci.
‘Yan majalisar jam’iyya mai mulki ta AK sun yi kokarin kafa kariya a kusa da Gurlek domin ba shi damar karanta rantsuwar kama aiki a cikin wannan yanayi na rudani.
"Wannan naɗi wani farmaki ne ga doka," in ji 'yan majalisar adawa yayin da suke ihu da sokar matakin da shugaba Erdogan ya ɗauka.

Source: Getty Images
Sauye-sauye na farko a majalisar ministoci
Wannan shi ne garambawul na farko da gwamnatin Erdogan ya yi tun bayan zaɓen tsakiyar shekarar 2023, inda Gurlek ya maye gurbin Yilmaz Tunc a matsayin Ministan Shari'a.
Haka kuma, Erdogan ya naɗa gwamnan lardin Erzurum, Mustafa Ciftci, a matsayin Ministan Cikin Gida, inda ya maye gurbin Ali Yerlikaya, in ji rahoton AP News.
Kodayake gwamnati ba ta bayar da takamaiman dalilin yin wannan garambawul ba, masu lura da al'amura suna ganin hakan a matsayin ƙarfafa iko ne ga shugaban ƙasar.
Gwamnati ta musanta zargin cewa tana amfani da shari'a wajen murƙushe adawa, inda take ikirarin cewa fannin shari'a na gudanar da ayyukansa ne ba tare da tsangama ba.
Kalli bidiyon rigimar da ta barke a majalisar, wanda @visionergeo ya wallafa a shafinsa na X:
An samu hargitsi a majalisar Najeriya
A wani labari, mun ruwaito cewa, rikici ya barke tsakanin Sanata Rufai Sani Hanga da Sanata Onyekachi Nwaebonyi yayin da ake gudanar da zaman kare kasafin kudi.
Takaddamar ta fara ne lokacin da Sanata Hanga ya katse Nwaebonyi yayin da yake yaba wa ministan ayyuka, David Umahi tare da kira ga abokan aikinsa su yi hakan.
Wannan sabani ya dakatar da zaman na dan lokaci kafin aka samu daidaito aka ci gaba da tattaunawa kan abubuwan da aka sanya a gaba a zaman.
Asali: Legit.ng


