Abu Ya Girma: Sarkin Saudiyya Ya Umarci Fita Sallar Rokon Ruwa a Masallatai 12,000
- Sarkin Saudiyya, Sarki Salman bin Abdulaziz, ya bayar da umarnin gudanar da sallar roƙon ruwa a duk faɗin ƙasar
- Sanarwar fadar Sarki ta ce za a gudanar da sallar a masallatai sama da 12,000 ciki har da Masallacin Harami da Masallacin Annabi
- Sarki Salman ya bukaci jama’a su tuba, su yawaita istigfari, tare da dogaro ga rahamar Allah domin shi kaɗai ke saukar da ruwan sama
Abdullahi Abubakar, Editan Legit Hausa ne ta bangaren siyasa, kasuwanci da al'amuran yau da kullum, ya na da gogewar aikin jarida sama da shekaru biyar.
Riyadh, Saudi Arabia - Mai kula da Masallatai Biyu Masu Alfarma, Sarki Salman bin Abdulaziz na kasar Saudiyya, ya bayar da umarnin gudanar da Sallar rokon ruwa.
Basaraken ya ce za a yi sallar a duk faɗin masarautar ranar Alhamis 12 ga Fabrairun 2026 da muke ciki inda ya roki al'umma su tuba tare da komawa ga Allah.

Source: Getty Images
Ruwan sama: Sarkin Saudiyya ya ba da umarni
Hakan na cikin wata sanarwa da Legit Hausa ta samu wanda shafin Inside The Haramain ya wallafa a X a jiya Talata 10 ga watan Fabrairun 2026.
Bisa ga umarnin da aka fitar daga fadar Sarki, an bukaci al’umma su koma ga Allah cikin ƙanƙan da kai, su nemi gafara tare da shirya tarukan addu’ar neman ruwan sama.
Sanarwar hukuma ta bayyana cewa za a gudanar da Sallar a masallatai sama da 12,000 a faɗin Saudiyya, ciki har da Masallacin Harami da Masallacin Annabi
Limamai za su jagoranci addu’o’i na musamman domin neman saukar ruwan sama, neman gafarar zunubai da kuma alherin al’ummar Musulmi gaba ɗaya.
Sanarwar ta ce:
"Mai Kula da Masallatan Harami Biyu Masu Tsarki, Sarki Salman bin Abdulaziz Al Saud, ya yi kira da a gudanar da sallar neman ruwa a fadin Masarautar Saudiyya a ranar Alhamis, 24 ga Sha’aban 1447 (12 ga Fabrairu, 2025)."

Source: Facebook
Sarki ya ja hankalin Musulmi kan tuba
Sarki Salman ya jaddada muhimmancin tuba da yawaita neman gafara a rayuwar Musulmi, yana mai cewa a dogara da rahamar Allah domin shi ne mai saukar da ruwa.
Ya ƙara da cewa Allah ne kaɗai ke ba ƙasa rai ta hanyar ruwan sama, don haka ya kamata jama’a su ƙarfafa imaninsu da fatan samun rahama.
An kammala shirye-shiryen tarukan sallar rokon ruwa a duk faɗin masarautar, inda ake sa ran miliyoyin jama’a za su halarta domin yin addu’a.
Ana tsammanin taron zai kasance cikin tsari a masallatai daban-daban, yayin da Musulmai za su roƙi Allah da zuciya ɗaya domin albarkar ruwan sama.
Giya: Saudiyya ta yi rangwame ga attajirai
Mun ba ku labari a baya cewa kasar Saudiyya ta fara bai wa attajiran baki da ba Musulmi ba damar sayen giya a Riyadh bayan haramci na tsawon shekaru 73.
Sabon tsarin ya shafi masu 'Premium Residency' ko wadanda ke samun albashi mai tsoka, yayin da baki masu yawon bude ido ba su cikin tsarin.
Masana na ganin matakin na daga cikin shirye-shiryen 'Vision 2030' domin jawo jari, kwararru da masu yawon bude ido a kasar baki daya.
Asali: Legit.ng


